Amurka ta ɗaure basaraken Osun kan zamba a tallafin COVID-19
Published: 27th, August 2025 GMT
Wata kotu a Ƙasar Amurka, ta yanke wa Sarkin Ipetumodu, Oba Joseph Oloyede, daga Jihar Osun, hukuncin ɗaurin shekara huɗu da rabi a gidan yari saboda samun sa da laifin zamba a tallafin COVID-19.
Alƙalin kotun, Christopher Boyko ne, ya yanke wa Sarkin mai shekara 62 a duniya hukunci a ranar 26 ga watan Agusta, 2025.
Sarkin ɗan ƙasar Amurka ne, da ke zaune a Ohio.
Bayan ya fito daga gidan yari, zai yi shekara uku ƙarƙashin kulawa, sannan dole ne ya biya sama da dala miliyan 4.4.
Kotun ta kuma ƙwace gidansa da ke Ohio da kusan dala 100,000 da aka samu daga cikin kuɗaɗen da aka yi bincike a kansu.
Waɗanda suka shigar da ƙara sun ce Oloyede tare da abokinsa, Edward Oluwasanmi, sun karkatar da kuɗaɗe wanda gwamnatin Amurka ta samar na rance don taimaka wa kamfanoni a lokacin annobar COVID-19.
Daga watan Afrilun 2020 zuwa Fabrairun 2022, sun gabatar da takardun bogi don samun rance ta hanyar U.S. Small Business Administration (SBA).
Oloyede, ya mallaki kamfanoni da ƙungiya mai zaman kanta, yayin da Oluwasanmi ya mallaki kamfanoni guda uku.
Oloyede, ya shirya takardun bogi 38 da suka ba shi damar samun dala miliyan 4.2.
Haka kuma, ya taimaka wa wasu abokansa wajen samun rancen, tare da karɓar kashi 15 zuwa 20 daga cikin kuɗin da suka samu a ɓoye, ba tare da ya biya haraji ba.
An gano cewa sun yi amfani da kuɗin wajen sayan filaye, gina gidaje, da kuma motoci masu tsada.
Oluwasanmi, wanda shi ma yake da shekara 62, an yanke masa hukuncin ɗaurin shekara biyu da watanni uku gidan yari a watan Yuli.
Sannan kotun ta umarci ya dawo da sama da dala miliyan 1.2.
FBI da wasu hukumomi ne suka gudanar da bincike tare da gano yadda aka tafka zamba a tallafin na COVID-19.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp