Aminiya:
2025-11-03@04:07:51 GMT

Yadda aka kama mutum 333 da muggan makamai a zaben Kano

Published: 19th, August 2025 GMT

Mutum 333 sun shiga hannu kan zargin aikata laifuka a yayin zaben cike gurbi da aka kammala a Jihar Kano.

A ranar Asabar aka gudnar da zaben na cike gurbi a mazabun Majalisar Tarayya da akamaimaita a ranar Asabar a mazabar Ghari/Tsanyawa da kuma zaben cike gurbi na Bagwai/Shanono.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ne ya sanar da karuwar adadin mutanen daga 288 a ranar Litinin a hedikwatar rundunar da ke Kano.

A cewarsa, zaben ya fuskanci barazana sakamakon “shigo da ’yan daba da dama daga cikin da wajen jihar” da suka yi yunkurin dagula tsarin zaben, amma an samu nasarar shawo kan lamarin ta hanyar haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

 

“An kama mutane 333 a yankunan Ghari, Bagwai da Shanono bisa zargin dagula tsarin zabe, kuma an kwato abubuwa da dama daga hannunsu,” in ji CP Bakori.

Hatsarin kwalekwale: An ceto mutane 26 ana neman 25 a Sakkwato  ’Yan bindiga sun yi hatsari bayan karbar kudin fansa Ya soka wa budurwarsa wuka har lahira

Ya ce abubuwan da aka kwato sun haɗa da bindigogi 6, gorori 94, takubba 16, adduna 18, barandami 32, wukake 18, baka da kibau 23, alburusai 45, motoci 14, akwatin zaɓe guda 2, takardun zaɓe da aka riga aka dangwala guda 163, da kuma kuɗi Naira 4,048,000.

Bakori ya ƙara da cewa duk waɗanda aka kama an gurfanar da su a kotuna kan zargin haɗin guiwar aikata laifi, tayar da hankali, mallakar makamai masu haɗari, tsoratarwa, yawo ba tare da dalili ba, satar kayan zaɓe da kuma neman ƙuri’a ta hanyar da ba ta dace ba.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare sahihancin tsarin zaɓe da tabbatar da cewa duk wanda ya yi yunkurin dagula shi zai fuskanci hukunci.

Ya yaba da ƙoƙarin hukumomin tsaro da ya bayyana da “ƙwarewa da sadaukarwa” a lokacin zaben, yana mai cewa hakan ne ya hana tashin hankali ya yadu.

Bakori ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bin doka da oda tare da ba da haɗin kai ga jami’an tsaro, yana mai jaddada cewa tsaro alhakin kowa ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ghari Jami an Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”

A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.

“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”

Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.

“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?