Aminiya:
2025-09-17@23:15:24 GMT

Yadda aka kama mutum 333 da muggan makamai a zaben Kano

Published: 19th, August 2025 GMT

Mutum 333 sun shiga hannu kan zargin aikata laifuka a yayin zaben cike gurbi da aka kammala a Jihar Kano.

A ranar Asabar aka gudnar da zaben na cike gurbi a mazabun Majalisar Tarayya da akamaimaita a ranar Asabar a mazabar Ghari/Tsanyawa da kuma zaben cike gurbi na Bagwai/Shanono.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ne ya sanar da karuwar adadin mutanen daga 288 a ranar Litinin a hedikwatar rundunar da ke Kano.

A cewarsa, zaben ya fuskanci barazana sakamakon “shigo da ’yan daba da dama daga cikin da wajen jihar” da suka yi yunkurin dagula tsarin zaben, amma an samu nasarar shawo kan lamarin ta hanyar haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

 

“An kama mutane 333 a yankunan Ghari, Bagwai da Shanono bisa zargin dagula tsarin zabe, kuma an kwato abubuwa da dama daga hannunsu,” in ji CP Bakori.

Hatsarin kwalekwale: An ceto mutane 26 ana neman 25 a Sakkwato  ’Yan bindiga sun yi hatsari bayan karbar kudin fansa Ya soka wa budurwarsa wuka har lahira

Ya ce abubuwan da aka kwato sun haɗa da bindigogi 6, gorori 94, takubba 16, adduna 18, barandami 32, wukake 18, baka da kibau 23, alburusai 45, motoci 14, akwatin zaɓe guda 2, takardun zaɓe da aka riga aka dangwala guda 163, da kuma kuɗi Naira 4,048,000.

Bakori ya ƙara da cewa duk waɗanda aka kama an gurfanar da su a kotuna kan zargin haɗin guiwar aikata laifi, tayar da hankali, mallakar makamai masu haɗari, tsoratarwa, yawo ba tare da dalili ba, satar kayan zaɓe da kuma neman ƙuri’a ta hanyar da ba ta dace ba.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare sahihancin tsarin zaɓe da tabbatar da cewa duk wanda ya yi yunkurin dagula shi zai fuskanci hukunci.

Ya yaba da ƙoƙarin hukumomin tsaro da ya bayyana da “ƙwarewa da sadaukarwa” a lokacin zaben, yana mai cewa hakan ne ya hana tashin hankali ya yadu.

Bakori ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bin doka da oda tare da ba da haɗin kai ga jami’an tsaro, yana mai jaddada cewa tsaro alhakin kowa ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ghari Jami an Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta shiga tsakani don sasanta rikicin da ya ɓarke tsakanin Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO).

Rikicin ya samo asali ne daga katse wutar lantarki da asibitin ya zargi KEDCO da yi, inda ya ce hakan ya kawo cikas ga ayyukan lafiya masu muhimmanci a asibitin, ciki har da zargin mutuwar marasa lafiya.

Sasantawar da Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya jagoranta ta biyo bayan zarge-zargen cewa katsewar wutar ta haddasa mutuwar wasu marasa lafiya da ke kan na’urar taimakon numfashi a asibitin.

Sai dai KEDCO ya musanta zargin a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, yana mai cewa asibitin na kokarin bata sunansa ne kawai.

A cewar mai magana da yawun ‘yan sanda na Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, an gudanar da taron sasancin ne a hedikwatar ‘yan sandan Kano da ke Bompai, inda aka zauna da Shugaban asibitin, Farfesa Abdulrahman Abba Sheshe, da Shugaban KEDCO, Abubakar Shuaibu Jimeta.

Taron ya mayar da hankali ne kan warware tankiyar da kuma dawo da wutar lantarki ga asibitin, wanda ke ya fuskanci matsaloli sakamakon katse wutar.

Sanarwar ta ce, “Bangarorin biyu sun nuna godiya ga matakin gaggawa da ‘yan sanda suka dauka. KEDCO ya amince da dawo da wutar lantarki nan take, alamar cewa rikicin ya zo karshe.”

Kiyawa ya kara da cewa, “Rundunar ‘Yan Sanda ta jaddada kudirinta na kare rayuka da dukiyoyi, tare da tabbatar da ci gaba da aiki ba tare da tangarda ba a bangaren kiwon lafiya.”

Sanarwar ta kuma ce kwamishinan ‘yan sanda ya yaba wa AKTH da KEDCO bisa hadin kai, tare da alkawarin ci gaba da goyon baya don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO