A jiya Talata ce babban zaureb MDD wanda yake da mambobi 188 a majalisar a jiya Talata sun zabi kasashen Bahrain, Colombia, Democradiyar Congo, Latvia,da Liberia don aiki a kwamin tsaro na Majalisar har zuwa shekara 2027.

Shafin yanar gizo na labarai ‘Afroca News” yace ana gudanar da zaben ne a cikin zagaye guda kacal na zabe.

Labarin ya kara da cewa kasashen zasu fara aiki a bangarin majalisar wanda yake da alhakin tabbatar da sulhu da zaman lafiya a duniya ne daga cikin watan Jenerun shekara ta 2026. Har zuwa karshen watan Dcemba na shekara ta 2027. Wato shekaru biyu cur.

Labarin ya kara da cewa a yankin Asiya dai an zabi Bahrain da kuri’u 186, sai kuma kasashen Afirka ina Demcdradiyyar Congo ta sami kuri’u 183 da kuma kasar Leberia da kuri’u 181, tare da kasa guda wacce ta ki kada kuri’arta. Sai Colombiya da kuri’u 180, inda 8 suka ki kada kuri’unsu.

Sannan kasar Latvia daga gabacin Turai  wacce ta sami kuri’u 178 tare da kasashe 10 da suka ki kada kuri’unsu. In banda kasar Latvia wacce take wannan aikin a karon farko, sauran kasashen sun sha aiki a kwamitin tsaro na MDD. Colombia sau 7, DRC sau 2, Bahrain da Liberia sun taba aikin har sau guda guda.

Kwamitin tsaro na MDD dai tana da mambobi na din-din din guda 5, kuma suna amurka, Rasha, China, Faransa da kuma Burtaniya. Sannan sauran kujeru 10 ana zaban sauran kasashen duniya su rike su na shekaru biyu-biyu. Sannan basu da hakkin Veto kamar na kasashen 5 da muka ambata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila suna da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila na da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi.

A yayin wani jawabi da ta gabatar a wajen juyayin tunawa da rasuwar Imam Khumaini {r.a}, Pezeshkian ya ce: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba za ta iya aikata wani aiki hauka da wauta ba, idan kasashen musulmi suka hada kansu.

Pezeshkian ya kara da cewa: Wadanda ke da’awar kare hakkin bil’adama suna kare “haramtacciyar kasar Isra’ila” mai laifi, kuma suna ci gaba da adawa da shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Ya ci gaba da cewa: “Babu mutum mai ‘yanci da zai yarda da zalunci da girman kai, kuma Iran ba zata yarda da shi ba.”

Pezeshkian ya bayyana cewa: “Za su dakile duk wani makirce-makircen abokan gaba kuma ba za su taba yin watsi da ‘yancinsu na nukiliya da na kimiyya ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya
  • Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu
  • Trump ya haramtawa ‘yan kasashen duniya 12 shiga Amurka
  • Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
  • Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
  • Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Mayar Da Martani Kan Bakar Siyasar Kwamitin Gwamnonin Hukumar IAEA
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran