Babban Zauren MDD Ta Zabi Kasashen Congo Da Liberian Na Zama Mambobi A Kwamitin Tsaro
Published: 4th, June 2025 GMT
A jiya Talata ce babban zaureb MDD wanda yake da mambobi 188 a majalisar a jiya Talata sun zabi kasashen Bahrain, Colombia, Democradiyar Congo, Latvia,da Liberia don aiki a kwamin tsaro na Majalisar har zuwa shekara 2027.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Afroca News” yace ana gudanar da zaben ne a cikin zagaye guda kacal na zabe.
Labarin ya kara da cewa a yankin Asiya dai an zabi Bahrain da kuri’u 186, sai kuma kasashen Afirka ina Demcdradiyyar Congo ta sami kuri’u 183 da kuma kasar Leberia da kuri’u 181, tare da kasa guda wacce ta ki kada kuri’arta. Sai Colombiya da kuri’u 180, inda 8 suka ki kada kuri’unsu.
Sannan kasar Latvia daga gabacin Turai wacce ta sami kuri’u 178 tare da kasashe 10 da suka ki kada kuri’unsu. In banda kasar Latvia wacce take wannan aikin a karon farko, sauran kasashen sun sha aiki a kwamitin tsaro na MDD. Colombia sau 7, DRC sau 2, Bahrain da Liberia sun taba aikin har sau guda guda.
Kwamitin tsaro na MDD dai tana da mambobi na din-din din guda 5, kuma suna amurka, Rasha, China, Faransa da kuma Burtaniya. Sannan sauran kujeru 10 ana zaban sauran kasashen duniya su rike su na shekaru biyu-biyu. Sannan basu da hakkin Veto kamar na kasashen 5 da muka ambata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
APC Ta Zabi Kamilu Sa’idu A Matsayin Dan Takarar Kaura Namoda Ta Kudu A Zamfara
Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ta zabi Hon. Kamilu Sa’idu (Wamban Kasuwar Daji) a matsayin dan takararta na Majalisar Dokokin Jihar Kaura Namoda ta Kudu da za a yi ranar 16 ga Agusta, 2025.
A wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya ce Kamilu ya fito ne ba tare da hamayya ba bayan janyewar wasu ‘yan takara uku Bashir Muhammad Madaro (Walin Kurya), Anas S/Fada, da Alhaji Ashiru Hamisu Habibu—a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka gudanar a makarantar firamare ta Kasuwar Daji.
Sanarwar ta ce, ‘yan takarar ukun sun sauka ne domin nuna goyon bayansu ga Kamilu Sa’idu inda suka yi alkawarin samun nasararsa da na jam’iyyar a zabe mai zuwa.
Ta ce an zabo wakilai 30 daga gundumomi shida na mazabar Kagara, Dan-Isa, Sakajiki, Kurya, Kyambarawa, da Banga — ya tabbatar da takararsa gaba daya.
Kwamitin zaben fidda gwani na jam’iyyar APC na kasa, karkashin jagorancin Barista Babande B. Imam ne ya jagoranci gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar, wanda a hukumance ya ayyana Kamilu Sa’idu a matsayin dan takarar jam’iyyar APC bayan da wakilan unguwanni suka amince da shi.
Barista Babande ya bayyana cewa dan takarar ya cika dukkan sharuddan tsarin mulki na jam’iyyar, kuma an tabbatar da shi a gaban jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), karkashin jagorancin kwamishina Dr. Muhammad Isah.
Bayan wannan sanarwa, shugaban kwamitin shari’a, Isah Halilu Ahmad, ya bayyana cewa idan akwai wani mai korafi dangane da sakamakon zaben fidda gwani ya fito yayi, kuma ba a sami wand ya gabatarda wani korafi ba domin duka masu neman takara da wakilai sun tabbatar da gamsuwarsu da tsarin.
Daga nan sai ya tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci, ba tare da wani magudi ba.
An gudanar da zagaye da manyan jagororin jam’iyyar da suka hada da shugaban jam’iyyar APC na jihar Zamfara, Hon. Tukur Umar Danfulani; Sakataren, Hon. Ibrahim Umar Dangaladima; Mataimakin shugaban kungiyar Alh. Hassan Marafa Damri da halartar jami’an tsaro da jami’an INEC.
REL/AMINU DALHATU.