A jiya Talata ce babban zaureb MDD wanda yake da mambobi 188 a majalisar a jiya Talata sun zabi kasashen Bahrain, Colombia, Democradiyar Congo, Latvia,da Liberia don aiki a kwamin tsaro na Majalisar har zuwa shekara 2027.

Shafin yanar gizo na labarai ‘Afroca News” yace ana gudanar da zaben ne a cikin zagaye guda kacal na zabe.

Labarin ya kara da cewa kasashen zasu fara aiki a bangarin majalisar wanda yake da alhakin tabbatar da sulhu da zaman lafiya a duniya ne daga cikin watan Jenerun shekara ta 2026. Har zuwa karshen watan Dcemba na shekara ta 2027. Wato shekaru biyu cur.

Labarin ya kara da cewa a yankin Asiya dai an zabi Bahrain da kuri’u 186, sai kuma kasashen Afirka ina Demcdradiyyar Congo ta sami kuri’u 183 da kuma kasar Leberia da kuri’u 181, tare da kasa guda wacce ta ki kada kuri’arta. Sai Colombiya da kuri’u 180, inda 8 suka ki kada kuri’unsu.

Sannan kasar Latvia daga gabacin Turai  wacce ta sami kuri’u 178 tare da kasashe 10 da suka ki kada kuri’unsu. In banda kasar Latvia wacce take wannan aikin a karon farko, sauran kasashen sun sha aiki a kwamitin tsaro na MDD. Colombia sau 7, DRC sau 2, Bahrain da Liberia sun taba aikin har sau guda guda.

Kwamitin tsaro na MDD dai tana da mambobi na din-din din guda 5, kuma suna amurka, Rasha, China, Faransa da kuma Burtaniya. Sannan sauran kujeru 10 ana zaban sauran kasashen duniya su rike su na shekaru biyu-biyu. Sannan basu da hakkin Veto kamar na kasashen 5 da muka ambata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)

Shugaban aksar Iran, Massoud Pezeshkian, ya bayyana cewa martanin sojojin kasarsa ga Isra’ila zai zama mafi muni idan hare-haren Isra’ilar suka ci gaba.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa dakarun gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran za su dauki kwararan matakan mayar da martani mai tsauri idan har gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da kai farmaki kan Iran.

“Masu da’awar kare hakkin bil’adama ba wai kawai suna goyon bayan zaluncin gwamnatin sahyoniyawa ba ne, har ma suna karfafa mata gwiwar aikata wadannan munanan ayyuka ta hanyar ba ta makamai da kayan aiki,” in ji shi.

Mr. Pezeshkian ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila da ke samun goyon bayan Amurka da kasashen yammacin Turai ta sabawa dukkanin dokokin kasa da kasa.

A nasa bangaren, firaministan Pakistan ya bayyana goyon bayan kasarsa ga al’ummar iran, yana mai yin Allah wadai da keta hurumin kasar Iran da ‘yancinta, wanda ya zama cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.

Sharif ya sake jaddada cewa Iran na da cikakken ‘yancin kare kanta a karkashin doka ta 51 na kundin tsarin mulkin MDD inda ya bayyana fatan ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev
  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai