Aminiya:
2025-07-23@22:34:17 GMT

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwana 10

Published: 2nd, June 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwanaki goma domin bikin Babbar Sallah da za a yi ranar Juma’ar wannan makon.

Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, a cikin wata sanarwa ta bayyana cewa makarantun za su fara hutun ne daga ranar Laraba, 4 ga watan nan na Yuni da muke ciki, zuwa ranar Lahadi, 15 ga wata.

Sanarwar ta kuma bukaci iyaye da ’ya’yansu suke makarantun kwana da su je da wuri domin daukar yaran a ranar Laraba.

Kwamishinan mai kula da ma’aikatar, Ali Makoda, ya kuma bukaci iyaye da su tabbata daliban sun dawo makaranta a kan kari bayan kare hutun Babbar Sallar.

An lakaɗa wa Mataimakin Firinsifal duka saboda hana satar a jarabawa Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara

A sakonta na taya daliban murna da fatan za a yi Babbar Sallah lafiya, ma’aikatar ilimin ta bayyana cewa hutun ya yi daidai da jadawalin zangon karatu da ake ciki, kuma ba a canza shi ba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babbar Sallah gwamnatin Kano makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce umurnin da sojojin Isra’ila suka bai wa Falasɗinawa na ficewa tsakiyar Gaza, babban koma baya ne ga ƙoƙarin ceton rayukan al’ummar yankin da yaƙi ya ɗaiɗaita.

A ranar Lahadi ne Isra’ila ta umarci Falasɗinawa a Deir el-Balah, da su koma kudancin Gaza saboda ayyukan soji.

MDD ta sake nanata gargaɗin da ta yi cewa al’ummar Gaza da dama na mutuwa saboda yunwa kuma suna buƙatar agajin abinci cikin gaggawa yayin da Isra’ila ke ci gaba da taƙaita shigar da kayan agaji.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati
  • DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye
  • MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi