Leadership News Hausa:
2025-06-03@11:57:16 GMT

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Published: 2nd, June 2025 GMT

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Ministan Muhalli, Barrister Mohammed Hassan Abdullahi, ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki a Nasarawa.

Abdullahi ya yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari a matsayin ƙaramin Minista na Kimiyya da Fasaha, kafin daga bisani ya zama cikakken Ministan Muhalli. Haka kuma, ya taɓa riƙe muƙamin Sakataren Gwamnatin Jihar Nasarawa a lokacin Gwamna Tanko Al-Makura.

Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano

Ya miƙa wasiƙar ficewarsa ga shugaban jam’iyyar APC na mazaɓarsa ta Uke, a ƙaramar hukumar Karu ta jihar Nasarawa, a ranar Lahadi. Wasikar ta nuna dalilinsa na barin jam’iyyar a matsayin na “ƙashin kai”.

Barrister Abdullahi ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta ba shi na yi wa ƙasa hidima da kuma goyon bayan da ya samu a lokacin aikinsa, inda ya ce: “Ina yi wa jam’iyya da shugabanninta fatan alheri.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nassarawa jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya gana da shugaban kasar Masar a birnin Alkahira

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi a yau Litinin.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arakchi ya isa birnin Alkahira da yammacin jiya Lahadi domin tattaunawa da manyan jami’an kasar Masar.

A yayin wannan ziyara, Araqchi ya gana da ministan harkokin wajen Masar Badr Abdel Aty da shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi inda suka tattauna batutuwan baya-bayan nan a dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da ci gaban yankin, musamman batun kalubalantar laifukan haramtacciyar kasar Isra’ila, da kuma wasu batutuwan kasa da kasa.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da Shirin ministan harkokin wajen Iran na ziyartar ministan harkokin wajen kasar Masar da Lebanon a wani taron manema labarai da ya kira a yammacin ranar Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana
  • Sabon Firay Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
  • Sabon Fira Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
  • Fira Ministan Kasar Senegal Yana Ziyarar Aiki A Kasashen Yammacin Afirka
  • Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
  • Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
  • Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi