Leadership News Hausa:
2025-11-03@03:09:28 GMT

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Published: 2nd, June 2025 GMT

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Ministan Muhalli, Barrister Mohammed Hassan Abdullahi, ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki a Nasarawa.

Abdullahi ya yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari a matsayin ƙaramin Minista na Kimiyya da Fasaha, kafin daga bisani ya zama cikakken Ministan Muhalli. Haka kuma, ya taɓa riƙe muƙamin Sakataren Gwamnatin Jihar Nasarawa a lokacin Gwamna Tanko Al-Makura.

Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano

Ya miƙa wasiƙar ficewarsa ga shugaban jam’iyyar APC na mazaɓarsa ta Uke, a ƙaramar hukumar Karu ta jihar Nasarawa, a ranar Lahadi. Wasikar ta nuna dalilinsa na barin jam’iyyar a matsayin na “ƙashin kai”.

Barrister Abdullahi ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta ba shi na yi wa ƙasa hidima da kuma goyon bayan da ya samu a lokacin aikinsa, inda ya ce: “Ina yi wa jam’iyya da shugabanninta fatan alheri.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nassarawa jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka

Daga Yusuf Zubairu Kauru 

Al’ummar Karamar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna sun shiga halin kaka-ni-ka-yi duba da yadda rayukansu ke kasancewa cikin hadari yayin da suke gonakinsu.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, wani jagoran matasa, Junaidu Ishaq, ya bayyana cewa kusan shekaru biyar ke nan da hare-haren ’yan bindiga ke ta faruwa akai-akai, wanda ya bar al’umma cikin fargaba da ƙuncin rayuwa.

Ya ce manoma suna shiga gonakinsu ne cike da fargaba domin komi na iya faruwa yayin da suke aiki a gonakin.

Mazauna yankin sun bayyana cewa Kauru, wadda aka fi sani da yawan gonaki da ke taka muhimmiyar rawa wajen samar da abinci a jihar Kaduna, yanzu manoma ba sa iya shiga gonakinsu cikin kwanciyar hankali saboda yadda ‘yan bindiga ke yawan kai musu hare-hare.

A koda yaushe iyayen yara suna fargaba kada ‘ya’yansu su yi nesa da su, yayin da iyalai da dama da ke fama da ƙangin talauci ke kara shiga cikin matsanancin hali.

Sun yi kira gwamnati da hukumomin tsaro su yi gaggawar kai ɗauki wanda zai bai wa manoman karkara kwarin gwiwa, waɗanda su ne ginshiƙin samar da abinci a yankin.

Mazaunan sun yi gargadin cewa idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, hare-haren na iya haifar da ƙaruwar matsalar rashin abinci da yawaitar ƙaura daga yankin.

“Idan zuwa gona zai sa mutumya rasa ransa, to lalle akwai babban matsala,” in ji wani manomi a yankin.

Sun yi fatan cewa za a dawo da zaman lafiya a yankin, yadda ƙasar da Allah Ya albarkace su da ita za ta ci gaba da ciyar da al’ummar Kauru ba wurin binne su ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP