An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka
Published: 21st, May 2025 GMT
An gudanar da taron dandalin tattaunawa na masanan Sin da Afirka karo na 14 a birnin Kunming dake lardin Yunnan na kasar Sin a yau Talata, 20 ga wata, inda wakilai kimanin 100 daga Sin da kasashen Afirka fiye da 50 suka halarci taron tare da tattauna fasahohin mulkin kasa da tafiyar da harkokin siyasa na kasar Sin da kasashen Afirka da kuma zamanintarwa irin ta kasar Sin.
Da yake tsokaci, Elia Kaiyamo, jakadan Namibia dake kasar Sin ya bayyana cewa, aikin zamanintar da kasa na da sarkakiya, domin kowace kasa tana da bambancin tarihi da al’adu da zamantakewar al’umma da tattalin arziki, don haka ya kamata a bi hanyoyi daban daban na zamanintarwa da suka dace da yanayin kasa, duk da cewa dukkansu suna da buri daya wato kyautata zaman rayuwar jama’a, da kawar da talauci, da raya zamantakewar al’umma mai inganci. Ya kara da cewa, fasahohin Sin na samun ci gaba sun shaida cewa, zamanintar da kasa tana da nasaba da bunkasuwar tattalin arziki, da sa kaimi ga samun daidaito a zamantakewar al’umma, da yi wa tsare-tsare kwaskwarima, da tafiyar da harkokin kasa yadda ya kamata.
A nasa bangare, shugaban kwalejin nazarin Afirka na kasar Sin Ye Hailin ya bayyana cewa, a matsayinsu na kasashe masu tasowa, Sin da kasashen Afirka suna kokarin zamanintar da kansu don samar da gudummawa wajen zamanintar da kasashe masu tasowa a duniya, da kuma kyautata harkokin jama’ar duniya baki daya. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: zamanintar da
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ta sha bamban da majalisun da ke goyon bayan masu goyon baya masu laifi misalin masu kisan gilla a Gaza
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada a yau Laraba cewa: Matsayin majalisar shawarar Musulunci ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya bambanta da kasashen duniya, kuma ya sha bamban da majalisar da ke goyon bayan zalunci, nuna wariya, banbance-banbancen ra’ayi da masu aikata laifuka irin su kisan gilla a Gaza.
Yayin ganawarsa da mambobin majalisar shawarar Musulunci a ranar Laraba, Jagora ya yi la’akari da cewa: Majalisun dokokin duniya suna da kamanceceniya ta fuskar nauyi doka. Duk da haka, ya jaddada cewa ma’auni na farko don kimanta taro shine ainihin nauyin su, watau, “manufofin su, alkiblar motsi, da matsayi.” Wannan shi ne ya sanya matsayin Majalisar Shawarar Musulunci ke da shi a duniya. A dabi’ance, ci gaba da wanzuwar wannan matsayi mai mahimmanci da daraja yana buƙatar yanayi da wajibai waɗanda dole ne membobin su kiyaye.
A farkon jawabin nasa, Ayatullah Khamenei ya bayyana Eid al-Ghadir a matsayin biki mai girma ga daukacin al’ummar musulmin duniya, mai cike da ilmin addinin Musulunci. Ya taya al’ummar Iran masu girma da alfahari murnar zagayowar wannan rana mai albarka, da kuma maulidin Imam Hadi (a.s). Ya dauki matakin shari’a na majalisun dokoki a kasashe na duniya a matsayin mai sanar da doka. Ya kara da cewa, “Dokar ita ce ainihin sharadi na zamantakewar bil’adama, kuma dokokin da tunani na gamayya da zababbun wakilan jama’a suka samar sun fi samun karbuwa da kima.” Jagoran ya yi nuni da cewa ma’auni na gaskiya na majalisu ya bambanta da juna, sabanin nauyinsu na shari’a. Ya ce, “Mataki da kimar majalisar da ta ginu a kan addini, wadda ta kunshi mutane masu tsoron Allah, masu gaskiya, ta mai da hankali kan adalci, da goyon bayan wadanda aka zalunta, da fuskantar azzalumai”.