Sarkin Saudiyya, Salman Bin Abdulaziz, ya bayar da umarnin ɗaukar nauyin Hajjin iyalan Falasɗinawa 1,000 da suka rasa ‘yan uwansu sakamakon yaƙin da ke ci gaba da gudana a Zirin Gaza da Isra’ila.

Wannan taimako na cikin littafin kujerun Hajji da masarautar ke rabawa a kowace shekara ga al’umma ko kuma ɗaukar nauyin waɗanda suka cancanta, ciki har da waɗanda suka riga suka biya kuɗin Hajjin.

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

Sarkin ya bayyana wannan mataki ne a matsayin ɗaya daga cikin hanyoyin nuna goyon baya da jin ƙai ga al’ummar Falsɗinawa a wannan lokaci mai wahala da suke ciki sakamakon yaƙi da ƙasar Yahudawa ta Isra’ila ta ƙaddamar a Gaza.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila

Wakilan kasashen duniya a Majalisar Dinkin Duniya sun nuna girmamawa ga wadanda suka yi shahada a harin wuce gona da irin yahudawan sahayoniyya kan Iran

Masu fafutukar wanzar da zaman lafiya da masu kiyayya da yaki na Amurka da wakilan kasashe daban-daban a Majalisar Dinkin Duniya sun gabatar da bayanai kan mutanen da suka yi shahada a hare-haren wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar kan kasar Iran ta hanyar halartar hedkwatar wakilan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya.

Daruruwan masu fafutukar neman zaman lafiya da masu kiyayya da yaki na Amurka ne suka hallara a hedkwatar tawagar Jamhuriyar Musulunci ta Iran da ke birnin New York a ranar Litinin din wannan mako don karrama shahidan harin da gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta kai kan kasar Iran, inda suka rattaba hannu kan littafin tunawa da nuna juyayi ga gwamnatin Iran da al’ummar kasarta.

Mambobin kungiyar Yahudawa ta kasa da kasa Neturei Karta, kungiyar Yahudawa masu adawa da ‘yan sahayoniyya, su ma sun halarci gangamin tare da nuna girmamawa ga wadanda harin ya rutsa da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
  • Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP
  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
  • Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba