Aminiya:
2025-06-20@07:16:01 GMT

Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa

Published: 5th, May 2025 GMT

Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan kan laifin kashe wata karuwa bayan ya yi lalata da ita.

Babban Kotun Jihar Ekiti ce ta yanke masa hukuncin bayan an gurfanar da shi kan zargin haɗa baki da kuma garkuwa da matar da kuma amfani da maganin kashe ciyawa wajen halaka ta a ranar 18 ga Afrilun 2024.

Tun da farko mai gabatar da ƙara, Ibironke Odetola, ya bayyana wa kotun a ranar 6 ga watan Fabrairu, cewa wanda ake zargin ya haɗa baki d da wani abokinsa wajen sace matar da ke sana’ar kasuwanci.

Wanda ake zargin, David Isaiah, mai shekara 26, ya shaida wa kotun cewa bayan ya yi lalata da matar ne ya yi amfani da wayarta ya kira abokan sana’arta da cewa an yi garkuwa da ita, sai an kawo kuɗin fansa Naira 100,000.

Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a Sakkwato Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki

A yayin da yake karanta hukuncin, Mai Shari’a Lekan Olatawura, ya yanke wa wanda aka gurfanar da laifin garkuwa da mamaciyar.

“Don haka an yanke masa hukuncin ɗaurin shekara 21 kan laifin haɗin baki kan laifin garkuwa da mutane. Game da laifin kisa kuma kotu ta yanke mas a hukuncin ratayewa har sai ya mutu,” in ji alƙalin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garkuwa Karuwa Rataye

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila

Kafofin yaɗa labarai na cikin gida a Iran sun yi iƙirarin cewa ƙasar ta kai hari kan hedikwatar hukumar leƙen asiri ta ƙasar Isra’ila (Mossad).

Kamfanin dillancin labaran Iran (TASNIM) ya ruwaito cewa rundumar juyin juya hali na Iran (IRGC) ce ta kai harin a hedikwatar Mossad da ke Herzliya.

Kamfanin ya wallafa wasu jerin hotuna da ya ce suna nuna yadda hedikwatar ta Mossad ke ci da wutan ne bayan harin makamai masu linzami ne da Iran ta kai mata.

Kafar yaɗa labarai ta Tehran Times ta ruwaito cewa hare-haren na IRGC sun ƙona wani ɓangare na cibiyar Aman, wanda wani ɓangare ne na ginin hukumar leƙen asirin asirin sojin Isra’ila ta Aman, da ke Glilot.

An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari

Kawo yanzu dai ba a iya tantance sahihancin wannan iƙirarin na Iran ba daga kafofin yaɗa labarai da ke aiki a yankin; kuma hukumomin Isra’ila ba su ce uffan a kai ba.

A cewar hukumar kare haƙƙin ɗan’Adam a Iran (HRANA), fararen hula 224 ne suka mutu, yayin da 188 suka jikkata a hare-haren Isra’ila a ƙasar.

HRANA ta kuma bayyana cewa sojoji 109 ne suka mutu inda kuma 123 suka jikkata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
  • Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
  • An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila