Aminiya:
2025-05-05@17:16:27 GMT

Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa

Published: 5th, May 2025 GMT

Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan kan laifin kashe wata karuwa bayan ya yi lalata da ita.

Babban Kotun Jihar Ekiti ce ta yanke masa hukuncin bayan an gurfanar da shi kan zargin haɗa baki da kuma garkuwa da matar da kuma amfani da maganin kashe ciyawa wajen halaka ta a ranar 18 ga Afrilun 2024.

Tun da farko mai gabatar da ƙara, Ibironke Odetola, ya bayyana wa kotun a ranar 6 ga watan Fabrairu, cewa wanda ake zargin ya haɗa baki d da wani abokinsa wajen sace matar da ke sana’ar kasuwanci.

Wanda ake zargin, David Isaiah, mai shekara 26, ya shaida wa kotun cewa bayan ya yi lalata da matar ne ya yi amfani da wayarta ya kira abokan sana’arta da cewa an yi garkuwa da ita, sai an kawo kuɗin fansa Naira 100,000.

Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a Sakkwato Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki

A yayin da yake karanta hukuncin, Mai Shari’a Lekan Olatawura, ya yanke wa wanda aka gurfanar da laifin garkuwa da mamaciyar.

“Don haka an yanke masa hukuncin ɗaurin shekara 21 kan laifin haɗin baki kan laifin garkuwa da mutane. Game da laifin kisa kuma kotu ta yanke mas a hukuncin ratayewa har sai ya mutu,” in ji alƙalin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garkuwa Karuwa Rataye

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan fashi sun kashe magidanci a Kano

Ana fargabar cewa wasu da ake zargin ’yan fashi ne sun kashe wani magidanci a  unguwar Ɗanbare da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Bayanai sun ce waɗanda ake zargin sun kashe magidancin ne da adda, bayan sun shiga gidansa da yake zaune domin sata da asuba.

To sai dai mazauna unguwar sun bayyana wa Aminiya cewa sun samu nasarar kama wanda suke zargin shugaban ’yan fashin ne, sun kuma miƙa shi ofishin ’yan sanda na Ɗorayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan fashi sun kashe matashi a Kano
  • ’Yan fashi sun kashe magidanci a Kano
  •  Kotun Duniya Ta Wanke HDL Akan Zargin Kisan Kiyashi A Sudan
  • PTAD Ta Dora Laifin Jinkirin Biyan Fansho Kan CBN, Ta Bukaci Hakuri
  • Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen
  • Yau Kotun ICJ ke yanke hukunci kan zargin da Khartoum ke wa UEA
  • An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi
  • Rudiger Zai Yi Jinyar Watanni Biyu