Mai shekara 92 ya shiga gasar Gudun Fanfalaƙi karo na 30 a jere
Published: 4th, May 2025 GMT
Gudu ya zamto wani bangare na rayuwar Antonio Rao tsawo dan kasar Italiya da yake da shekara 80, wanda yanzu yake da shekara 92, inda ba shi da shirin daina shiga gasar tsere.
A bana, ya kammala gasar gudun fanfalaƙi na Rome karo na 30 a jere cikin kasa da sa’o’i bakwai.
Ɗan shekara 19 da ya ƙirƙiro na’urar gano bam cikin daƙiƙa ɗaya Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’addaIdan mutum yana bukatar samun karin kuzari to ya shiga gasar gudu, wanda a kwanan nan wani dattijo mai shekara 92 ya kammala gudun fanfalaƙi na Roma na tsawon kilomita 42 a karo na 30 a jere, inda ya kara a kan bara da mintuna 10.
Antonio Rao yana horar da kansa gudun kilomita 20 zuwa 30 a kowane mako.
An haife shi a 1933, ya gudu daga gidansa a Calabria zuwa Roma a lokacin yana dan shekara 10 kuma bai daina gudu ba har zuwa yanzu.
Ya yi ikirarin cewa, yana gudu kowace rana tun yana matashi don ci gaba da kasancewa tare da abokinsa, wanda ya zama wani bangare rayuwarsa, kuma bai taɓa gaza shiga tseren Rome ko sau daya ba a cikin shekaru 30 da suka gabata.
“Idan zan iya yin hakan a wannan shekarun, kowa zai iya,” in ji Rao.
“Ina so in zama misali ga kowa.”
A wannan shekarar, Antonio Rao ya ƙetare layin ƙarshe na gasar tseren Marathon ta Rome a cikin sa’o’i 6 da mintuna 44 da daƙiƙa 16, wanda a zahiri ya kara kwazon da ya yi a bara da minti 10.
A ƙarshe ya ba da mamaki, amma babban nasarar da Antonio ya yi ita ce ci gaba da kasancewa a ƙarshen 2023, lokacin da ya kafa sabon tarihin a duniya na rukunin shekarunsa sama da 90.
Ya kammala tseren gudun fanfalaƙi cikin sa’o’i 6 da minti 14 don shiga kundun tarihin gasar dattawa ’yan shekaru 90 na duniya da minti 30 mai ban mamaki.
“Ba na jin daɗi kwanan nan, kuma ban yi tunanin zan iya kammala gasar ba, kuma a maimakon haka na kammala ta minti goma kasa da ta bara,” Rao ya shaida wa kafar yada labarai ta Runners World Italia bayan kammala gasar Marathon ta Rome ta bana.
“Tseren gudun, tafiyar rayuwa ce. Ina gayyatar kowa da kowa ya yi.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Antonio Rao Italiya
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
“Siyasar da na sani ba ita ce abin da ke faruwa a yau ba. Siyasar da na sani ita ce gwagwarmayar muradun jama’a don tabbatar da cewa suna da kyakkyawar rayuwa a duk fannoni kamar ilimi, ruwa, kiwon lafiya, da sauransu. “Na kasance a siyasa tsawon shekaru 48 da suka gabata,” in ji shi.
Ya bayyana yanayin siyasa a matsayin wanda ke cike da rudani da son kai, yana mai jaddada cewa ‘yan siyasa da talakawa sun rikice.
“Saboda wannan, akwai rudani ga masu nema da kuma wadanda ake nema. Masu neman suna makancewa, ba su da imani ko tausayi. Manufarsu kawai ita ce tabbatar da matsayi a gare su. A halin yanzu, talakawa sun tsunduma ciki yunwa, talauci, da jahilci, don haka komai yana cikin rudani,” in ji Bafarawa.
Tsohon gwamnan ya kuma nuna matukar damuwa game da karuwar jahilci a tsakanin matasa, musamman a arewacin Nijeriya, yana mai gargadin cewa makomar yankin na cikin hadari.
“Duk lokacin da kuka cusa mutane cikin jahilci ta hanyar hana su ilimi, kun gama da su. A nan arewa, a gaskiya, kusan kashi 70 cikin 100 na matasanmu ba su da ilimi. Ta yaya wata kasa ko yanki za ta ci gaba ba tare da ilimi ba?” ya tambaya.
Bafarawa ya kare talakawa masu jefa kuri’a da ke karbar kudi a lokacin zabe, yana mai cewa mawuyacin halin tattalin arziki da suke fuskanta ya sa ba su da wani zabi.
A cewarsa, taimakon Allah ne kadai zai iya ceto Nijeriya daga kalubalen da take fuskanta a yanzu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp