Mai shekara 92 ya shiga gasar Gudun Fanfalaƙi karo na 30 a jere
Published: 4th, May 2025 GMT
Gudu ya zamto wani bangare na rayuwar Antonio Rao tsawo dan kasar Italiya da yake da shekara 80, wanda yanzu yake da shekara 92, inda ba shi da shirin daina shiga gasar tsere.
A bana, ya kammala gasar gudun fanfalaƙi na Rome karo na 30 a jere cikin kasa da sa’o’i bakwai.
Ɗan shekara 19 da ya ƙirƙiro na’urar gano bam cikin daƙiƙa ɗaya Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’addaIdan mutum yana bukatar samun karin kuzari to ya shiga gasar gudu, wanda a kwanan nan wani dattijo mai shekara 92 ya kammala gudun fanfalaƙi na Roma na tsawon kilomita 42 a karo na 30 a jere, inda ya kara a kan bara da mintuna 10.
Antonio Rao yana horar da kansa gudun kilomita 20 zuwa 30 a kowane mako.
An haife shi a 1933, ya gudu daga gidansa a Calabria zuwa Roma a lokacin yana dan shekara 10 kuma bai daina gudu ba har zuwa yanzu.
Ya yi ikirarin cewa, yana gudu kowace rana tun yana matashi don ci gaba da kasancewa tare da abokinsa, wanda ya zama wani bangare rayuwarsa, kuma bai taɓa gaza shiga tseren Rome ko sau daya ba a cikin shekaru 30 da suka gabata.
“Idan zan iya yin hakan a wannan shekarun, kowa zai iya,” in ji Rao.
“Ina so in zama misali ga kowa.”
A wannan shekarar, Antonio Rao ya ƙetare layin ƙarshe na gasar tseren Marathon ta Rome a cikin sa’o’i 6 da mintuna 44 da daƙiƙa 16, wanda a zahiri ya kara kwazon da ya yi a bara da minti 10.
A ƙarshe ya ba da mamaki, amma babban nasarar da Antonio ya yi ita ce ci gaba da kasancewa a ƙarshen 2023, lokacin da ya kafa sabon tarihin a duniya na rukunin shekarunsa sama da 90.
Ya kammala tseren gudun fanfalaƙi cikin sa’o’i 6 da minti 14 don shiga kundun tarihin gasar dattawa ’yan shekaru 90 na duniya da minti 30 mai ban mamaki.
“Ba na jin daɗi kwanan nan, kuma ban yi tunanin zan iya kammala gasar ba, kuma a maimakon haka na kammala ta minti goma kasa da ta bara,” Rao ya shaida wa kafar yada labarai ta Runners World Italia bayan kammala gasar Marathon ta Rome ta bana.
“Tseren gudun, tafiyar rayuwa ce. Ina gayyatar kowa da kowa ya yi.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Antonio Rao Italiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar SDP a zaben 2023, Adewole Adebayo, ya ce Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ba shi da burin da ya wuce na tara haraji tun yana Gwamna a Legas.
Adebayo ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels.
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin NajeriyaA cewarsa, “Kowa ya san cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu sananne ne wajen karbar haraji. Amma wannan tsarin karbar haraji ya fi tsarin da ya tarar da shi wanda ba shi da tsari.
“Ya yi hakan a Legas, sannan ya zo Abuja domin ya dora daga inda ya tsaya a Legas.”
Sai dai Adebayo ya ce Tinubu ya yi kokari wajen bunkasa tattalin arzikin Najeriya.
“A bayyane yake cewa tattalin arzikin da Shugaba Buhari ya bari ba a tafiyar da shi yadda ya kamata ba, kuma yana cikin mawuyacin yanayi kamar na mara lafiya da aka kai dakin jinya. Kamar yadda likita ke bukatar yin cikakken bincike domin gano matsalar mara lafiyan, haka ma ake bukatar fahimtar matsalar tattalin arziki kafin a fara warkar da ita.
“Abin da Shugaba Tinubu ya yi shi ne ya daidaita marar lafiyan, amma ban tabbatar ko ya kai ga gano matsalar ba. Don haka mara lafiyar ba zai mutu nan da nan ba, amma kuma ba a samo maganin cutar shi ba.
“Ba a gano ciwon da ke damun mara lafiyan ba, amma a matsayinsa na likita, yana daukar wasu matakai. Wasu daga cikin matakan ma sun kara ciwon mara lafiyar, amma sannu a hankali likitan yana samun nasara a wasu bangarorin, wanda hakan ke sa wasu su yi tunanin cewa mara lafiyan na kan hanyar warkewa,” in ji Adebayo.