HausaTv:
2025-06-18@13:53:39 GMT

An Daure Tsohon Fira Ministan Kasar Tunisiya Shekaru 34 A Kurkuku

Published: 3rd, May 2025 GMT

 Wata kotu a kasar Tunisiya ta daure tsohin fira minsitan kasar Ali al-Aridh zaman kurkuku na tsawon shekaru 34

Shi dai al-Aridhi wanda dan jami’iyyar masu kishin musulunci ta ‘al-Nahdha’ ya zama fira minista ne daga shekarar 2013 zuwa 2014.

Kotun ta zargi tsohon Fira ministan da hannu a ayyukan ta’addanci, lamarin da shi da jam’iyyar tasa su ka kore.

A cikin  makwannin bayan nan dai ana yanke wa ‘yan adawa hukuncin dauri, lamarin da masu fafutuka suke dauka a matsayin bita da kulli na siyasa da shugaba Kais Sa’id yake yi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima

An samu saɓani a wani taron shugabannin jam’iyyar APC a yankin Arewa Maso Gabas da aka gudanar a Jihar Gombe.

Rikicin ya fara ne bayan da Kwamared Mustapha Salihu, Mataimakin Shugaban APC na ƙasa mai kula da Arewa Maso Gabas, ya bayyana goyon bayansa ga takarar Shugaba Bola Tinubu don ya sake tsayawa takara a karo na biyu.

Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

Sai dai bai ambaci mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ba.

Manyan jiga-jigan jam’iyyar APC daga yankin sun halarci taron, ciki har da gwamnoni, ministoci, da ‘yan majalisa.

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, shi ma ya halarci taron.

Bayan Salihu ya gama jawabi, wasu daga cikin mahalarta taron sun fusata.

Take suka fara yi masa ihu, wasu ma suna barazanar kai masa hari.

Sai jami’an tsaro sun fito da shi daga ɗakin taron don kare lafiyarsa.

Don kwantar da rikicin da ya taso, Mataimakin Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Bukar Dalori, ya fito ya bayyana goyon baya ga Tinubu da kuma Shettima don su ci gaba da mulki.

Amma lamarin ya ƙara dagulewa bayan da Ganduje ya yi jawabi, inda ya ayyana goyon bayansa ga Tinubu kaɗai, ba tare da ya ambaci Shettima ba.

A yayin jawabin da ya yi na kusan minti 10, bai ambaci sunan Shettima ba.

Shi ma sai da jami’an tsaro suka fita da shi daga wajen taron saboda gudun rikicin da zai je ya dawo.

Shettima dai ɗan Jihar Borno ne, ɗaya daga cikin jihohin yankin Arewa Maso Gabas.

Mutane da dama sun ji ba ɗadi kan rashin ambaton sunan a wajen taro da aka yi a yankinsa.

Taron ya kare cikin gaggawa saboda tashin hankali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575
  • Palermo ta ɗauki Filippo Inzaghi
  • Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda
  • Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara
  • Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya
  • PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima