Aminiya:
2025-11-03@01:59:26 GMT

Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Gabon

Published: 3rd, May 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai bar Abuja yau zuwa Libreville, babban birnin ƙasa Gabon, domin ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Brice Clotaire Oligui Nguema.

A halin yanzu Shugaba Tinubu yana ziyara ta kwanaki biyu a Jihar Katsina.

A cewar Stanley Nkwocha, mai magana da yawun Mataimakin Shugaban Kasa, Najeriya na goyon bayan sauyin mulki na dimokuraɗiyya cikin lumana a ƙasar Gabon kuma ta sake tabbatar da ƙudirinta na inganta dimokuraɗiyya a Afirka.

Oligui Nguema, wanda ya kasance shugaban riƙon ƙwarya na Gabon tun watan Agustan 2023, ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a ranar 12 ga Afrilu, inda ya samu kashi 94.85% na ƙuri’un da aka kaɗa.

Rashin tsaro: ‘Ba za mu miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba’ Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara

’Yan takara bakwai ne suka fafata, inda tsohon Firayim Minista Alain Claude Bilie-By-Nze ya zo na biyu da kashi 3%.

Ana sa ran Shettima zai dawo Najeriya bayan bikin rantsarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dimokuraɗiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.

Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.

Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.

Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.

Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.

Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi? October 31, 2025 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta