Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Gabon
Published: 3rd, May 2025 GMT
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai bar Abuja yau zuwa Libreville, babban birnin ƙasa Gabon, domin ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Brice Clotaire Oligui Nguema.
A halin yanzu Shugaba Tinubu yana ziyara ta kwanaki biyu a Jihar Katsina.
A cewar Stanley Nkwocha, mai magana da yawun Mataimakin Shugaban Kasa, Najeriya na goyon bayan sauyin mulki na dimokuraɗiyya cikin lumana a ƙasar Gabon kuma ta sake tabbatar da ƙudirinta na inganta dimokuraɗiyya a Afirka.
Oligui Nguema, wanda ya kasance shugaban riƙon ƙwarya na Gabon tun watan Agustan 2023, ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a ranar 12 ga Afrilu, inda ya samu kashi 94.85% na ƙuri’un da aka kaɗa.
Rashin tsaro: ‘Ba za mu miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba’ Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara’Yan takara bakwai ne suka fafata, inda tsohon Firayim Minista Alain Claude Bilie-By-Nze ya zo na biyu da kashi 3%.
Ana sa ran Shettima zai dawo Najeriya bayan bikin rantsarwar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dimokuraɗiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita
Kafin ya yi ritaya daga Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya, AVM Kaita ya riƙe muƙamai da dama, ciki har da Daraktan Tsare-tsare a Hedikwatar Tsaro da kuma Shugaban Sashen Kirkire-Kirkire na tsaro.
Ana girmama shi saboda gudunmawar da ya bayar wajen horarwa da inganta ayyukan rundunar sojin sama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp