An kama matashi kan ‘satar’ ’yar maƙwabcinsa
Published: 2nd, May 2025 GMT
An kama wani matashi ɗan shekaru 33 bisa zargin yin garkuwa da ’yar maƙwabcinsa mai shekaru 21 a ƙauyen Paikon Bassa da ke Ƙaramar Hukumar Abaji a yankin Babban Birnin Tarayya.
Wani ɗan banga a yankin, Dangana Bala, ya ce an kama wanda ake zargin ne bayan samun ƙorafi daga iyayen matashiyar da ta ɓace na wasu makonni.
Ya ce iyayenta sun yi zargin mutumin, wanda suka ce ya daɗe yana soyayya da ita a ɓoye.
Ya ƙara da cewa da samu wannan bayanin, ’yan sintirin suka sanar da abokan aikinsu a ƙauyen Dafa da ke makwabta da su, kuma an gano matashiyar a ƙauyen Tukurwa da ke Ƙaramar Hukumar Kwali a ranar Lahadin da ta gabata.
Wulaƙancin da ake mana a Kudu ya yi yawa —Hausawan Legas NAJERIYA A YAU: Yadda naira biliyan ɗaya ta salwanta a gobarar Kasuwar JosYa ce ’yan sintirin sun gano cewa a ranar da ake shirye-shiryen Easter, mutumin ya fita da yarinyar a kan babur ya kai ta gidan abokinsa a ƙauyen.
“A gaskiya, iyayen yarinyar sun daɗe suna korafin cewa mutumin ya jima yana soyayya da ita a ɓoye. Har ma sun gargade ta da ta nisanci mutumin. A ranar Lahadi, ’yan sintirinmu da ke Dafa sun ga yarinyar da mutumin a kan babur, kuma nan take suka sanar da mu, muka je ƙauyen Tukurwa don kama shi a gidan abokinsa.”
Sun kuma ce tun farko mutumin ya musanta ɗauke yarinyar lokacin da iyayenta suka je wurinsa suna neman inda take.
Ya ce, “Daga baya mun samu labarin cewa ya fi shekara yana soyayya da ita da niyyar aure, amma iyayenta sun ƙi duk da cewa ya kashe kuɗi a kanta.”
Bala ya ce an miƙa mutumin da abokinsa da aka samu yarinyar a gidansa, ga jami’an tsaro a Kwali.
’Yan sanda a yankin sun tabbatar da faruwar lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Garkuwa makwabtaka soyayya
এছাড়াও পড়ুন:
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”
Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”
Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.
“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.
Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.
Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.
Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.
“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.
“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA