An kama matashi kan ‘satar’ ’yar maƙwabcinsa
Published: 2nd, May 2025 GMT
An kama wani matashi ɗan shekaru 33 bisa zargin yin garkuwa da ’yar maƙwabcinsa mai shekaru 21 a ƙauyen Paikon Bassa da ke Ƙaramar Hukumar Abaji a yankin Babban Birnin Tarayya.
Wani ɗan banga a yankin, Dangana Bala, ya ce an kama wanda ake zargin ne bayan samun ƙorafi daga iyayen matashiyar da ta ɓace na wasu makonni.
Ya ce iyayenta sun yi zargin mutumin, wanda suka ce ya daɗe yana soyayya da ita a ɓoye.
Ya ƙara da cewa da samu wannan bayanin, ’yan sintirin suka sanar da abokan aikinsu a ƙauyen Dafa da ke makwabta da su, kuma an gano matashiyar a ƙauyen Tukurwa da ke Ƙaramar Hukumar Kwali a ranar Lahadin da ta gabata.
Wulaƙancin da ake mana a Kudu ya yi yawa —Hausawan Legas NAJERIYA A YAU: Yadda naira biliyan ɗaya ta salwanta a gobarar Kasuwar JosYa ce ’yan sintirin sun gano cewa a ranar da ake shirye-shiryen Easter, mutumin ya fita da yarinyar a kan babur ya kai ta gidan abokinsa a ƙauyen.
“A gaskiya, iyayen yarinyar sun daɗe suna korafin cewa mutumin ya jima yana soyayya da ita a ɓoye. Har ma sun gargade ta da ta nisanci mutumin. A ranar Lahadi, ’yan sintirinmu da ke Dafa sun ga yarinyar da mutumin a kan babur, kuma nan take suka sanar da mu, muka je ƙauyen Tukurwa don kama shi a gidan abokinsa.”
Sun kuma ce tun farko mutumin ya musanta ɗauke yarinyar lokacin da iyayenta suka je wurinsa suna neman inda take.
Ya ce, “Daga baya mun samu labarin cewa ya fi shekara yana soyayya da ita da niyyar aure, amma iyayenta sun ƙi duk da cewa ya kashe kuɗi a kanta.”
Bala ya ce an miƙa mutumin da abokinsa da aka samu yarinyar a gidansa, ga jami’an tsaro a Kwali.
’Yan sanda a yankin sun tabbatar da faruwar lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Garkuwa makwabtaka soyayya
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.