Aminiya:
2025-09-18@00:53:58 GMT

Gwamnonin Arewa maso Gabas sun buƙaci a ɗauki mataki kan matsalolin yankin

Published: 2nd, May 2025 GMT

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya yaba wa takwarorinsa na gwamnonin Jihohin  Borno, Bauchi, Adamawa, Gombe da Taraba a bisa ga samun damar da suka yi na halartar taron ƙungiyarsu ta Arewa maso Gabas (NEGF) karo na 11 a garin Damaturu.

Ya yi wannan yabo ne a ranar Alhamis a ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Damaturu yayin jawabinsa na maraba yadda ya  bayyana fatansa cewa, taron zai samar da sabbin dabarun yaƙi da rashin tsaro da taɓarɓarewar tattalin arziki.

Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas Gobara ta lalata shagunan kasuwar waya a Kwara

Buni ya bayyana wannan ƙungiyar a matsayin wani muhimmin dandali na haɗin gwiwa da daidaita manufofi, musamman yadda yankin ke fama da sabbin hare-hare daga ƙungiyar Boko Haram da kuma amfani da fasahar zamani wajen kai hare-hare.

“Wannan taron ya zo kan lokaci. Dole ne mu yi aiki da sauri don ƙarfafa nasarorin da muka samu wajen gina zaman lafiya da farfaɗo da tattalin arziki,” in ji shi.

Ya yi kira da a raba ƙudurori daga taron da hukumomin tsaro na tarayya domin bunƙasa haɗin kai da hanyoyin mayar da martani cikin gaggawa.

Gwamna Buni ya kuma nuna jin daɗinsa ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa goyon bayansa da jagoranci, sannan ya mika godiyarsa ga rundunonin sojan ƙasar, rundunar hadin gwiwa ta farar hula da masu aikin sa kai bisa sadaukarwar da suka yi.

A kan farfaɗo da tattalin arziki, ya yi kira wajen neman saka hannun jari a harkar noma, samar da ayyukan yi da kuma shirye-shiryen rayuwa mai ɗorewa.

“Dole ne mu sanya aikin noma ya zama abin sha’awa, mai araha, kuma mai riba don amfani da albarkatun ƙasa da na ɗan Adam,” in ji shi.

Ana sa ran taron zai fitar da ƙudurori da nufin ƙarfafa ayyukan tsaro na haɗin gwiwa, da daidaita ayyukan jin ƙai da inganta kasuwanci da zuba jari a yankin.

Yayin da yankin ke ci gaba da bin hanyoyin farfaɗowa, hakan ya sake tabbatar da abu guda: hanyar samar da zaman lafiya da walwala wadda  ta ta’allaka ne a cikin haɗin kai da hangen nesa da aiki tuƙuru.

Da yake jawabin maraba ga gwamnonin na Arewa maso Gabas wajen wannan taron shugaban Ƙungiyar gwamnnonin Arewa maso Gabas Farfesa Babagana Umara Zulum na Jihar Borno ya bayyana irin ƙalubalen da wannan yanki ke fuskanta dangane da harkokin tsaro da kuma talauci, yadda ya nemi al’ummomin yankin da su yi ƙoƙari wajen ganin an samu canji.

Ya kara da cewa, akwai buƙatar da haɗa kai don ganin an samu nasarar wajen shawo kan wannan matsala ta dawo da taɓarɓarewar harkokin tsaro a wannan yanki wadda kuwa babbar matsala ce.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Taraba Arewa maso Gabas

এছাড়াও পড়ুন:

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

A bayan bayan nan, an aiwatar da jerin tattaunawa tsakanin Sin da Amurka karkashin jagorancin shugabanninsu, inda aka samu kyawawan sakamakon da ya kyautata alakarsu ta tattalin arziki da cinikayya. Wannan ya nuna shawarar da a kullum Sin ke bayarwa cewa, tattaunawa ita ce mafita ga dukkan rikice-rikice, maimakon amfani da karfi.

Kasar Sin ta sha nanata cewa, babu mai samun nasara a yakin cinikayya ko haraji. Mun ga yadda aka samu hauhawar farashin kayayyaki da karuwar rashin aikin yi da faduwar darajar hannayen jari a Amurka, a lokacin da ta kaddamar da yakin haraji, wanda ya nuna cewa, maimakon cimma abun da take fata na samun fifiko, asara aka samu da lalacewar muradun kamfanoni da ’yan kasuwar kasar.

Kowace kasa tana da cikakken iko da ’yancin zabar manufofi da matakan da ya dace da ita. Da Sin ta tsaya kai da fata cewa ba za ta ba da kai a yakin haraji da Amurka ta tayar ba, hakan ya sa Amurka yin karatun ta nutsu, kuma ta tuntubi bangaren Sin domin tattaunawa.

Wadannan misalai sun nuna mana cewa, akwai hanyoyi masu sauki da inganci na samun maslaha, kuma shawarwarin da Sin take gabatarwa, su ne suka dace da yanayin duniya a yanzu. Ba dole sai kowa ya samu abun da yake so ba, amma hawa teburin sulhu da tuntubar juna tana taka muhimmiyar rawa wajen warware sabani, da lalubo inda kowane bangare zai iya saki, domin a samu mafitar da za ta karbu ga kowa. Kuma irin wannan din, shi ne burin sabuwar Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar a baya bayan nan. Duniya ba ta bukatar mayar da hannu agogo baya ta hanyar tayar da rikice-rikice da danniya da nuna fin karfi, zamani ya sauya kuma dole salon tafiyar da harkoki ya sauya, domin dacewa da yanayin da ake ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila