Aminiya:
2025-07-31@02:02:09 GMT

Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji

Published: 24th, April 2025 GMT

Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Olufemi Oluyede, ya ba wa dakarun rundunar wa’adin wata guda su fatattaki sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta Mahmud a da ta ɓulla a Jihar Kwara.

Oluyede ya ba da wannan umarnin ne a lokacin da yake jawabi ga sojojin a ziyarar da ya kai Barikin Sobi da ke Ilorin, babban birnin jihar.

“Daga wata mai zuwa, ba na son in ƙara jin mostin waɗannan ’yan ta’addan a yankin Dam ɗin Kainji,” in ji babban hafsan sojin.

Ya umarce su da su kawar da ’yan ta’addan daga ƙananan hukumomi biyun da suka addaba, yana mai jaddada cewa yana son a kammala aikin cikin wata mai zuwa.

Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa gidan rediyo na haɗin gwiwa NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci

Babban hafsan sojin ya ce Najeriya ba za ta iya ba da damar ’yan fashin daji ko ’yan ta’adda su ƙara yaɗuwa zuwa wani ɓangare na ƙasar ba.

“Don haka, kuna nan kuma na san za ku yi hakan don tabbatar da cewa waɗancan mutanen sun bar mana wannan wurin,” kamar yadda ya shaida wa sojojin.

“Idan suna son shiga wata ƙasa, wannan su ta shafa, amma dole ne ku kawar da su daga waɗannan dazuzzukan don kada mu sake samun wata ƙungiyar Boko Haram da za ta dame mu a nan.

“Ina iya gaya muku, cikin wata mai zuwa, al’amura za su bambanta. Abin da ke faruwa a Kwara ba zai iya yin barazana ga zaman lafiyar Najeriya gaba ɗaya ba; lamari ne keɓantacce kuma za mu magance shi kai tsaye.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya
  • Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe
  • NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INEC