Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan
Published: 22nd, April 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su shirya zanga-zangar nuna goyon baya ga Gaza da kuma kin amincewa da kisan kare dangi
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su tashi tsaye wajen gudanar da gangami da zanga-zanga a ranar Talata, domin nuna goyon baya ga Gaza, da tsayin dakanta, da kuma kawo karshen kisan kiyashi.
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, shugaban kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bukaci ‘yan Falasdinu gami da daliban jami’o’in Falasdinu masu ‘yanci a Yammacin Gabar Kogin Jordan da suke mamaye da su da su tashi tsaye tare da gudanar da zanga-zangar bacin rai da aka shirya za a fara a yau Talata, domin nuna goyon baya ga zirin Gaza da kuma yin watsi da yakin da ake yi na kawar da al’ummart yankin.
Jagora Shadid ya jaddada cewa, dole ne kungiyar dalibai a yammacin gabar kogin Jordan ta taka rawa wajen dakatar da kisan kiyashi da kuma daukar matakan gaggawa ga Gaza a dukkanin fagagen jama’a da jami’o’i, yayin da ake ci gaba da yakin kisan kiyashi da kuma fatattakar da ‘yan gwagwarmaya suke ci gaba da gwabza fada a fagen yakin ambaliyar al-Aqsa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
Adadin mutanen da suka yi shahada sakamakon kisan kiyashin da ‘yan sahayoniyya suke yi a Gaza ya doshi 65,000
Adadin mutanen da suka yi shahada sakamakon yakin da yahudawan sahayoniyya suka kakaba wa Falasdinawa a yankin Zirin Gaza ya karu zuwa shahidai 64,871 da kuma jikkatan wasu 164,610 tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023.
Bisa kididdigar baya-bayan nan da ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta fitar a zirin Gaza a ranar Lahadin da ta gabata, mutane 12,321 ne suka yi shahada yayin da wasu 52,569 suka samu raunuka tun bayan da gwamnatin mamayar Isra’ila ta sake komawa yaki kan Falasdinawa a ranar 18 ga watan Maris.
A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, Falasdinawa 68 ne suka yi shahada tare da jikkatan wasu 68 da aka isa da su zuwa asibitocin Gaza.
Haka nan wasu Falasdinawa 10 sun yi shahada wasu 18 kuma suka jikkata da aka kai su asibitoci, lamarin da ya kawo adadin wadanda hare-haren ta’addancin ya rutsa da su a cikin bala’in neman tallafin abinci suka haura zuwa shahidai 2,494 da kuma wasu fiye da 18,135 da suka samu raunuka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci