Aminiya:
2025-07-31@19:14:40 GMT

An jingine wasanni a Italiya saboda mutuwar Fafaroma Francis

Published: 21st, April 2025 GMT

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Italiya, FIGC, ta sanar da jingine wasannin gasar gasannin Serie A, B, da C, saboda alhinin rasuwar shugaban ɗarikar Katolika, Fafaroma Francis.

Shugaban hukumar FIGC, Gabriel Gravina ya ce, “Harkar ƙwallon ƙafa ta Italiya tana taya jimami ga miliyoyin al’umma kan rasuwar Mai Alfarma Fafaroma Francis.

Ƙungiyoyin da dakatarwar ta shafa sun haɗa da Juventus, Lazio, Parma Calcio, Cagliari, Fiorentina, Genoa, Torino, Udinese.

A safiyar Litinin 21 ga Afrilu ne Fadar Cocin Katolika da ke Vatican City ta sanar da rasuwar Fafaroma Francis mai shekaru 88, wanda ke shugabantar Cocin, kuma shugaban birnin Vatican City.

Miliyoyin mutane a Italiya da kuma faɗin duniya sun shiga alhini saboda rasuwar malamin adinin.

Wannan ya sa aka ɗauki matakin jingine duka lamuran wasanni don nuna girmamawa ga rasuwar.

An soke duka wasannin da aka shirya bugawa ranar Litinin ta Easter, inda a babbar gasar Serie A ta Italiya, Juventus za ta kara da Parma, Lazio da Genoa, Torino da Udinese, Cagliari da Fiorentina.

Haka ma a ƙananan gasannin Italiya na Serie B da Serie C su ma an soke buga wasannin da aka tsara a baya.

Hukumar ta FIGC ta fitar da sabon jadawali da ke nuna cewa za a buga wasannin a ranar 23 ga wannan watan.

A halin yanzu dai galibi ƙungiyoyin suna da sauran wasanni biyar ne kafin kammala kakar gasanni ta bana.

Tarihi ya nuna cewa ko a 2005 da Fafaroma John Paul II ya rasu, an ɗauki irin wannan mataki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fafaroma Francis Italiya Wasanni Fafaroma Francis

এছাড়াও পড়ুন:

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wadannan ’yan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi sun sake nuna bajintar da kasar Sin ke nunawa a fagen kere-keren mutum-mutumi masu siffar dan’adam da kuma yadda masana’antar bangarensu ke samun ci gaba cikin hanzari a kasar.

A watan Agusta mai kamawa ne kasar Sin za ta karbi bakuncin gasar wasannin motsa jiki na mutum-mutumi masu siffar dan’adam. Kuma wannan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi da aka gwabza fafatawar karshe a dandalin wasannin motsa jiki na fasahar zamani da ke birnin Beijing, wata kyakkyawar shaida ce a kan yadda kasar ta shirya wa karbar bakuncin wannan gasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
  • EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci