Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama
Published: 21st, April 2025 GMT
Sai dai Bukarti wanda ya shafe shekaru da dama yana gudanar da bincike kan kungiyar ta ‘yan ta’adda, ya kara nuna fargabar cewa, a halin yanzu ‘yan tada kayar bayan na yaɗa aƙidarsu a shafukan sada zumunta ta hanyar ɗora naɗaɗɗen faifan bidiyo da kuma gabatarwa kai tsaye.
Ya ce, “Yanzu idan ka shiga TikTok, za ka ga shafukan ‘yan Boko Haram, suna gudanar da shirye-shirye kai-tsaye ko kuma su ɗora naɗaɗɗen bidiyo, inda suke yada akidar Boko Haram, suna kafa hujjar kashe-kashen da suke yi da harshen Hausa, suna amsa tambayoyi daga masu sauraro, suna amsa tsokaci da aka rubuta.
“Ko a wannan makon ma, an samu wani dan Boko Haram da ya saka wani bidiyo na mintuna 10 a TikTok yana kai min hari saboda na yi magana kan karuwar ta’addancin kungiyar, amma ba wannan kadai ba, mun san cewa Boko Haram a yanzu suna sarrafa jirage marasa matuka, suna sa ido kan tsarin soja a yankin arewa maso gabas da jirage marasa matuka.
“Abin da muka gani cikin watanni uku da suka wuce shi ne hare-hare bakwai da ‘yan Boko Haram suka kai a manyan ssansanonin a sojojin Nijeriya. A Sabon Gari da sauran wurare da dama sun mamaye sansanonin, sun tarwatsa sojoji, sun kashe wasu, sannan sun kama wasu, suka sace makamai, abinci, magunguna da sauran kayan aiki daga yankunan, suka gudu cikin daji.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Boko Haram Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.
Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.
Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.
Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.
Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.
Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA