Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi
Published: 19th, April 2025 GMT
Dubban jama’a ne suka hallara domin ɗaurin auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi a Fadar Mai Martaba Sarkin Bauchi ciki har da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima da Ministan Lafiya, Farfesa Mohammed Ali Pate, da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Yusuf Tuggar.
Cikin baƙi akwai Shugaban Kamfanin rukuin Media trust Malam Kabiru Yusuf da sauran manyan baƙi suka hallara a birnin domin ɗaurin auren da kuma naɗin sarautar “Makama Babba I da aka yi wa tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Mohammed Abdullahi Abubakar.
Alhaji Bala Ahmad babban limamin Bauchi ne ya jagoranci ɗaurin auren, wanda Shettima ya kasance a matsayin waliyyin ɗiyar tsohon gwamnan yayin da Yusuf Yakubu Wanka, Chigarin Bauchi, ya kasance waliyyin angon, Sadiƙ Mohammed Wanka a wajen ɗaurin auren.
Bayan ɗaurin auren, Sarkin Bauchi, Alhaji Rilwanu Suleimanu Adamu ya naɗa wa tsohon gwamnan rawani a matsayin Makama Babba na farko, sannan ya sa baƙar Alkyabba.
Tun da farko mataimakin shugaban ƙasar, wanda ya sauka a filin jirgin sama na Sa Abubakar Tafawa Balewa ya samu tarba daga gwamnan jihar, Sanata Bala Mohammed da gwamnan Jihar Gombe Mohammed Inuwa Yahaya.
Haka kuma, taron ya samu halartar wasu manyan baƙi da dama, ciki har da tsohon gwamnan jihar Bauchi, Ahmadu Mu’azu, mataimakin gwamnan Yobe, Shugaban Kamfanin Media Trust Malam Kabiru Yusuf da sarakunan gargajiya da jama’a daga kowane fanni.
Fadar Sarkin dai ta cika maƙil a yayin da sauran manyan baƙi daga sassa daban daban su ma suka halarci bikin, inda aka ɗaura auren Sadiƙ Mohammed Wanka, da Khadijatu Mohammed Abdullahi Abubakar akan sadakin Naira 300,000.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed ya bayyana godiyarsa ga Shettima, Pate, Tuggar da Gwamnan Jihar Gombe da sauran manyan baƙi bisa halartar ɗaurin auren da kuma bikin naɗin sarautar tsohon Gwamna a matsayin Makama Babba na Bauchi na farko.
Ya kuma taya tsohon Gwamnan murna kan abin da ya bayyana a matsayin mafi kyawu kuma wanda ya cancanta saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sadiƙ Mohammed Wanka tsohon gwamnan tsohon Gwamnan Gwamnan Jihar ɗaurin auren gwamnan Jihar manyan baƙi
এছাড়াও পড়ুন:
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
“Ana kiransa da suna dokar binciken tntanet ta tsoratarwa, wadda kasashen da suka ci gaba da dama suka dade da yin watsi da ita. A karni na 21, ba za a iya tunanin cewa gwamnatin Nijeriya za ta tauye ‘yancin fadin albarkacin baki, wanda shi ne ginshikin mulkin dimokuradiyya.”
Atiku ya ce duk wata doka da ke take ‘yancin ‘yan kasa na yin tsokaci mai muhimmanci game da shugabanninsu ko a hanyoyin sadarwar zamani ko ta hanyar magana ba dimokuradiyya ba ce kuma kai tsaye take hakkokin Dan’adam ne.
“A cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata tun bayan da gwamnatin Tinubu ta fara daukan matakan da ke janyo kuncin tattalin arziki da yunwa da bakin ciki ga mutanen Nijeriya, mun shaida zanga-zanga da koke-koke daga ‘yan kasa da ba za su iya daukar mulkin rashin gaskiya ba. Duk da haka, maimakon sauraron ‘yan kasa sai gwamnatin ta zabi hanyar amfani da karfin hukumo da tsoratarwa wadda ta juya lamarin zuwa wani abu daban.
“Lallai abin bakin ciki ne na ganin ana take hakkin ‘yan kasa da kundin tsarin mulki ya tabbatar a lokacin da ya kamata dimokuradiyyarmu ta kasance mai bin tsari. Dole ne mu tunatar da gwamnatin Tinubu cewa babu gwamnati a lokacin da ta kasa kare ‘yancin ‘yan kasarta, komai karfinta kuwa. Yin haka abun ta da hankali ne kuma hakan yana nuna gazawar gwamnati a fili.”
Atiku ya ce tabbas gwamnati na da alhakin kula da doka da oda, babu ingantacciyar gwamnati da za ta harbi masu zanga-zangar lumana da harsashi mai rai ko ta boye a bayan dokoki tana musguna wa ‘yan kasa.
Ya ce rashin kulawar gwamnati Tinubu ga dokar kasa da kuma ci gaba da kin bin umarnin kotu sun zama shahararrun siffofinta mafiya suna a kasar nan a halin yanzu.
Tsohon mataimakin shugaban kasa ya kara da cewa tun farkon wannan gwamnati, kungiyar kare hakkin Dan’ada ta Amnesty ta soke wannan gwamnatin da take hakkin Dan’adam.
Ya ce haka ma wasu kungiyoyi masu muhimmanci kamar irinsu kungiyar ‘yan jaridu ta Nijeriya da kungiyar kare ajandar kafafen yada labarai sun yi korafi kan cin zarafin ‘yan jarida da ‘yan kasa ta hannun jami’an gwamnati.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA