Leadership News Hausa:
2025-07-31@14:31:50 GMT

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Published: 19th, April 2025 GMT

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

To mun san ki a matsayin marubuciyar littafan Hausa. Shin ta ya kika tsinci kanki a duniyar rubutu?

Hukuncin Ubangiji, na yi karance-karance da dama a baya, tun ina karamar secondary na fara rubuta labari a paper a shekarar 2016, idan na rubuta sai na ajiye. Lokacin da muka yi hutu da aka dawo aji na Hudu (a kasar Nijar shekara 4 muke yi a karamar secondary) a karamar secondary a lokacin na fara karantawa kawayena, idan an yi break, to bayan na gama karama secondry na ci gaba da rubutun a paper, a shekara ta 2019 na fara rubutu a yanar gizo har na fara yadawa.

A 2016 mene sunan littafin da kika fara rubutawa?

Gaskiya ba zan iya tunawa ba, don a lokacin ban wani kware a rubutu ba, bayan na gama karanta musu na kan nemi shawararsu a kan yadda labarin zai ci gaba ko abin da ya dace na canza ko sunan da ya dace da labarin.

To wanda kin fara yadawa a yanar gizo cikin shekaran 2019, wanne littafi ne?

Khairat: sunan littafin da na fara fitarwa a 2019 shi ne KHAIRAT. Labarin ya ginu ne don jan kunne ga irin iyayen da suke nacewa sai ‘ƴarsu ta yi karatu kuma a kasashen waje, sai a yi rashin sa’a ita kuwa yarinyar aure take son yi, daga nan rayuwar yaran za ta iya lalacewa, duk da ita Khairat din a nata bangaren ta yi aure ne a boye ba tare da sanin iyayenta ba a kasar da suka aika ta karatu. To bayan Khairat kuma zuwa yanzu na yi wasu littafan guda (14) har da shi ya zama ina da littafai (15) ke nan da na fitar, kuma dukkansu a yanar gizo. Littafan guda Goma Sha Biyar kuwa su ne: Khairat, Nazi’at, Na Yi Asara, Babbar ‘Yar Duniya, Dan Kuka, Mutuwar Aure, Samha, Tura Ta Kai Bango, Gudun Tsira, Dambarwar Aurensu, Dambarwar Abin Dake Raina, Kuskure, Da Wata Kusan, Abin Dake Boye, Kwakwalwar Kifi.

A cikin wadannan littafai guda 15, wanne ne bakandamiyarki?

Labarin ‘Kuskure’ shi ne bakandamiyata. Labari ne da aka gina shi a kan gudun son zuciya, cire kiyayyar wani mutum a rai saboda ba ka san abin da gobe za ta haifar ba. Don gaba da kiyayya ba su da amfani, kuma Manzon Rahama ma ya hane mu a kan zurfafawa a cikin kiyayya.

Kika ce a baya kin yi karance-karancen littafan Hausa. To cikin marubuta na wancan lokacin wace ce gwanarki?

To ai ni har yanzu ban daina karance-karancen Hausa ba. Duk da asalin marubutan sun daina rubutun zube, amma an samu sabbin marubuta. A da gwanata ita ce marubuciya Fauziyya D Sulaiman. A yanzu kuwa zabin tilo a cikin marubuta gare ni zabi ne mai wahala. Sai dai zan iya cewa: a bangaren zamantakewa marubuciya ‘Billyn Abdul’ ce gwanata, idan kuma bangaren horror sai na ce ‘Chamsiya Laouli Rabo’ idan kuma littafin yaki ne to marubuci ‘Mansur Usman Sufi’.

To ko cikin marubuta kina da kawa shakikiyar da kowanne lokaci za a iya samun labarin halin da keki ciki a wajenta?

Kwarai ina da Aunty Fa’iza Abubakar wadda aka fi sani da Maman Afrah.

To ya batun kungiyar marubuta?

Ina cikin kungiyar First Class Writer’s Association wadda tun farkon fara rubutuna antyna Rahama Sabo Usman ita ce ta saka ni a cikinta.

To a matsayinki na tsohuwar makaranciya, ya za ki kimanta marubutan da da kuma na yanzu ta fuskar kwarewa da ilimantarwa?

Babu hadi gaskiya domin kowa akwai matsayinsa, marubutan da sun yi rubutu ne a kan matsalolin da suka shafi al’umma a da, su kuwa marubutan yanzu suna rubutu ne a kan abin da ta shafe mu yanzu, duk da dai yanzu bin ka’idodi da dokokin da adabi ta tanadar ya yi karanci fiye da da can baya saboda yanzu duk wanda ya ga dama zai iya zama marubuci, sai kuma baragurbin marubuta wato marubutan batsa da suka yi yawa a halin yanzu wanda muna tufka su kuwa suna warware wa ne.

To ya batun shiga gasar rubutu?

A duk lokacin da zan ji labarin gasar rubutu bana kasa a guiwa wajen shiga, wasu an yi nasara wasu kuwa ba a yi ba, duk da dai iya shiga gasar ma nasara ce babba. Gasar da na yi nasara kuwa. Akwai gasar da aka shirya a lokacin bikin marubuci Yareema Shaheed gaskiya na manta sunan gidan tb da suka shirya gasar. Sai gasar da kungiyar raya al’adu ta jihar Gombe suka shirya.

Kuma a wanne yanayi ko lokaci kika fi jin dadin yin rubutu?

A duk lokacin da na ci na koshi bana kuma tare da gajiya, sha’awar yin rubutun kan zo mini.

To wadanna nasarori kika cimma a rayuwa ta sanadiyyar rubutu?

Na farko babbar nasara ta ita ce haduwa da mutanen kirki wanda a halin yanzu suke tamkar ‘yan uwana kama daga marubuta har makaranta.

Nasara ta biyu kuma harkar rubutu na saka ni alfahari don a duk inda zan shiga bana jin shakkar kiran kaina da marubuciya. A yanzu kuma bayan fadakarwar da nake yi ina daukar harkar rubutu a matsayin hanyar da zan samu dan na kashewa saboda bunkasar tattalin arzikina.

To wanne kalubale kika fuskanta bayan shigowar ki duniyar rubutu?

Da farko dai kalubalen da na fuskata daga mahaifiyata ne don ina fama da matsalar ciwon ido a lokacin idan na zauna na fara rubutun a waya ko laptop, za ta rika faka a kan ba ki da lafiya amman kullum kina jone da wannan screen ɗin don yin rubuce-rubuce, amman daga baya da rashin lafiyar ya yi sauki sai kawai ta daina mita tana yi min fatan alkairi. Kalubale na gaba kuwa ina son makaranta su rika yi min comment a duk bayan da suka karanta labarina sai dai kuma ba sa yi sai an kai ruwa rana.

Ko wanne kira za ki yi ga ‘yan uwanki marubuta?

Kirana ba zai wuce mu ji tsoron Allah a duk sanda za mu kaura alkalami ba, mu rubuta abin da zai anfane mu ya anfani al’umma, abin da ko da an tambaye ki gobe ba za ki yi da-na-sanin rubuta shi ba, kuma abin da ko ‘ƴarki ko kawarki za ki iya bari ta karanta. Sannan mu rike zumunci da karfafa juna ta hanyar karawa juna sani a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, domin duk inda marubuci yake to fa dan uwanmu ne. Sai kuma marubutan batsa ku ji tsoron Allah.

To wanne sako kike da shi ga masoyanki da suke bibiyar rubuce-rubucenki?

Ina yi wa duk wani masoyina fatan alkairi, da fatan Allah Ya biya masa bukatunsa na alkairi kuma ina mai farin cikin sanar da su zan ci gaba da fadakar da su da kuma nishadantar da su gwargwadon iyawata.

To Hajiya Emilia muna godiya.

Ni ce da godiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Marubuta

এছাড়াও পড়ুন:

An fara shigar da kayan agaji a Gaza

An fara shigar da kayyakin agaji zuwa Zirin Gaza wadanda galibi ta sararin samaniya aka rika jefawa da jirage daga kasashen Jordan da Hadaddiyar Daular Larabawa.

Arshiyan Kohen, kakakin ma’aikatar tsaron Isra’ila ya ce, za a dakatar da farmakin soji na tsawon sa’o’i 10 a kowace rana a wasu sassan Gaza tare da ba da damar samun sabbin hanyoyin ba da agaji.

DW ya ruwaito cewa ana ci gaba danka kayayyakin tallafin a hannun kungiyoyin agaji na kasa da kasa da suke ci gaba da ayyukan rarrabasu.

Tinubu ya bai wa ’yan ƙwallon Nijeriya mata kyautar kuɗi da gida da lambar yabo An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Gutteress ya siffanta wannan matakin da mai sanyaya zuciya bayan damuwa da bala’in da mazauna Gaza suka tsinci kansu a ciki, yana mai fatar gaggauta shigar da kayayyakin agajin da kuma dorewarsa.

A yayin taron tattaunawa kan matsalolin da suke shafar ayyukan samar da abinci a Afrika ne Guterres ya faɗi  cewa yunwa ba za ta taɓa zama makamin da za a yi amfani da ita wajen yaƙi a duniya ba.

Babban jami’in bayar da agajin gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya, Tom Fletcher ya yi maraba da matakin, yana mai cewa yanzu haka yana tuntubar kungiyoyi wadanda za su yi duk mai yiwuwa don isa ga mutane da dama da ke fama da yunwa a wannan lokaci.

Tuni dai kungiyoyin agaji suka gabatar da wasu korafe-korafe tun ba a yi nisa ba, don yi wa tufkar hanci muddin ana son kwalliya ta biya kudin sabulu a ayyukan agajin da aka fara bayan fiye da watanni uku da dakatar da su.

Ahmad Nadir, na kungiyar lafiya ta duniya WHO, ya ce tsame hannun Isra’ila daga batun karba da rabon kayan agaji ne kadai zai bai wa kwarraru kan ayyukan agaji damar gudanar da ayyukan da za a samu nasara.

A bayan nan ne Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya WFP ta ce kashi uku na al’ummar Gaza ba su ci abinci na kwanaki ba, kuma mutane 470,000 suna cikin yanayi na juriyar tsananin yunwa wanda tuni ya kai ga mutuwar wasu.

Isra’ila dai na ci gaba da fuskantar suka daga kasashen duniya, kan amfani da yunwa a matsayin makamin yaki kan al’ummar Falasdinu, lamarin da gwamnatin kasar ta ki amincewa da shi.

Akwai yunwa ta gaske a Gaza —Trump

Ko a wannan ɗin Litinin Shugaban Amurka Donald Trump ya ce “akwai yunwa ta gaske” a Gaza.

Shugaban na Amurka ya faɗi hakan ne bayan Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nace kan cewa babu yunwa a yankin.

Da aka tambaye shi ko ya yarda da abin da Netanyahu ya fada cewar “ƙarya ce tsagwaronta” idan aka ce Isra’ila na ta’azzara yunwa a Gaza, shugaban na Amurka ya ce: “Ban sani ba…amma yaran nan da ka gan su, suna cikin yunwa…wannan yunwa ce ta gaske.”

Kalaman Trump na zuwa ne bayan shugaban hukumar kai agaji ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce ana buƙatar abinci mai “ɗimbin yawa” domin magance halin yunwa da yankin ke ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza