Sojojin Sudan sun sanar da kashe mayakan dakarun kai daukin gaggawa 70, ciki har da kwamandojin mayakan a birnin a El Fasher fadar mulkin jihar Darfur ta Arewa

A ranar Alhamis ne rundunar sojin Sudan ta sanar da kashe mayakan da jami’an dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces fiye da 70 da suka hada da kwamandojin ‘yan tawaye a shiyar kudu maso gabas da arewa maso gabashin El Fasher.

Kamfanin dillancin labaran Sudan (SUNA) ya watsa rahoton cewa: A ranar Alhamis ne sojojin kasar Sudan tare da hadin da tallafin dakarun hadin gwiwa na kungiyoyin fafutuka, da hukumar leken asiri ta kasar da ‘yan sanda, suka dakile wani mummunan hari da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kaddamar kan shiyar kudu maso gabas da arewa maso gabashin El Fasher.

Majiyar ta tabbatar da cewa artabun ya yi sanadin lalata motocin yaki guda 15, da motocin dakon mai. Ta kuma tabbatar da cewa, an samu nasarar lalata da dama daga cikin motocin mayakan Dakarun Rapid Support Forces ciki har da manyan jami’an rundunar da yawansu ya haura 70 da suka hada da kwamandoji da dama baya ga wani adadi mai yawa da suka jikkata, yayin da sauran suka gudu, inda suka bar matattu da wadanda suka jikkata a filin daga.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa

Aƙalla mutum tara ne suka rasu, yayin da wani kwale-kwale ɗauke da fasinjoji 17 ya kife a Jihar Jigawa.

Yawancin fasinjojin da hatsarin ya rutsa da su ’yan mata ne.

Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres

Lamarin ya faru ne da ranar yammacin Lahadi, 27 ga watan Yuli, 2025, lokacin da kwale-kwalen ya taso daga ƙauyen Digawa a Ƙaramar Hukumar Jahun zuwa ƙauyen Zangon Maje da ke Ƙaramar Hukumar Taura.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis.

Ofishin NEMA na Kano, ya bayyana cewa kwale-kwalen ya kife ne a tsakiyar kogin.

Wasu mazauna yankin sun ceto mutum takwas da ransu, sai dai an yi rashin sa’a mutum tara sun riga mu gidan gaskiya.

NEMA tare da haɗin gwiwar Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (JSEMA), Hukumar Kula da Hanyoyin Ruwa ta Ƙasa (NIWA), da jami’an Ƙaramar Hukumar sun wayar da kan al’umma kan muhimmancin bin ƙa’idojin tsaro yayin tafiya a ruwa.

NIWA, ta kuma raba wa mutanen yankin rigunan kariya na ruwa don kare kansu daga irin wannan hatsari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
  • Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno