Adadin wadanda suka mutu sakamakon luguden wuta da Amurka ta yi kan tashar jiragen ruwan Ra’as Issa ta Yemen ya kai mutane 38

Ofishin kula da kiwon lafiya na lardin Al Hudaidah ya watsa rahoton cewa: Adadin mutanen da suka yi shahaida da wadanda suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai kan cibiyar man fetur ta Ra’as Issa da ke lardin Al-Hudaidah a yammacin kasar Yemen ya karu zuwa shahidai 38, tare da jikkata sama da mutane 100.

A yammacin jiya alhamis ne rundunar kawancen da Amurka ke jagoranta ta aikata wani mummunan laifi kan fararen hula a gundumar Al-Hudaidah da ke yammacin kasar Yemen.

Majiyoyin cikin gida sun shaidawa Al Masirah Net cewa: Jiragen yakin kawancen da Amurka ke jagoranta sun kai hare-hare 14 a kan tashar Ra’as Issa da ke gundumar, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu ma’aikata a wurin.

Majiyoyin sun yi nuni da cewa: An sake sabunta kai harin a wurin a yayin da jami’an tsaron farin kaya ke kokarin kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su, lamarin da ya yi sanadin shahadar jami’an tsaro da dama tare da jikkata wasu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.

Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.

Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49