Amurka Ta Kashe Mutane 38 Tare Da Jikkata Fiye Da 100 A Harin Da Ta Kai Lardin Al-Hudaidah Na Yemen
Published: 18th, April 2025 GMT
Adadin wadanda suka mutu sakamakon luguden wuta da Amurka ta yi kan tashar jiragen ruwan Ra’as Issa ta Yemen ya kai mutane 38
Ofishin kula da kiwon lafiya na lardin Al Hudaidah ya watsa rahoton cewa: Adadin mutanen da suka yi shahaida da wadanda suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai kan cibiyar man fetur ta Ra’as Issa da ke lardin Al-Hudaidah a yammacin kasar Yemen ya karu zuwa shahidai 38, tare da jikkata sama da mutane 100.
A yammacin jiya alhamis ne rundunar kawancen da Amurka ke jagoranta ta aikata wani mummunan laifi kan fararen hula a gundumar Al-Hudaidah da ke yammacin kasar Yemen.
Majiyoyin cikin gida sun shaidawa Al Masirah Net cewa: Jiragen yakin kawancen da Amurka ke jagoranta sun kai hare-hare 14 a kan tashar Ra’as Issa da ke gundumar, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu ma’aikata a wurin.
Majiyoyin sun yi nuni da cewa: An sake sabunta kai harin a wurin a yayin da jami’an tsaron farin kaya ke kokarin kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su, lamarin da ya yi sanadin shahadar jami’an tsaro da dama tare da jikkata wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
Sai dai don neman cimma burinta na “sake mayar da kasar Amurka zakaran gwajin dafi”, kasar Amurka ta sha daukar matakai na dakile ci gaban kasar Sin, ciki har da katse huldar tattalin arziki da ita da ma sanya takunkumai ga kamfanoninta masu ci gaban kimiyya da sauransu, duk da hakan, kasar Sin ta kiyaye bunkasar tattalin arzikinta yadda ya kamata, har ma karuwar tattalin arzikinta ta kai kaso 5.2% a cikin watanni tara na farkon bana, lamarin da ya shaida inganci da juriya na tattalin arzikin kasar. A kwanan nan, kasar Sin ta zartas da shawarwarin da aka gabatar game da tsara shirin raya tattalin arziki da zaman al’umma cikin shekaru biyar masu zuwa, kuma bisa ga shawarwarin, za a tsara shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15 na kasar. Cikin sama da shekaru 70 da suka wuce, kasar Sin ta yi ta kokarin aiwatar da shirye-shiryen ba tare da kasala ba, ba don neman kalubalantar wata ko maye gurbinta ba, amma don mai da hankali a kan raya kanta da kuma bayar da damammaki na samun ci gaba ga sauran kasashen duniya.
Ganawar da aka yi a wannan karo ta kasance ta farko a tsakanin shugabannin kasashen biyu tun bayan da shugaba Trump ya sake hawa karagar mulkin kasar Amurka. Kafin wannan kuma, shugabannin biyu sun taba tattaunawa da juna ta wayar tarho har sau uku, don nuna alkiblar bunkasar huldar kasashensu. Tun bayan watan Mayun da ya gabata, bisa daidaiton da shugabannin biyu suka cimma, tawagogin kasashen biyu sun gudanar da shawarwarin tattalin arziki da cinikayya har sau biyar. A sabon zagayen shawarwarin da aka gudanar a baya bayan nan a birnin Kuala Lumpur, sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan tattalin arziki da ciniki da ke janyo hankulansu duka, tare da cimma matsaya daya a kan matakan da za a dauka. Lallai ta hanyar yin shawarwari da juna cikin daidaito, sassan biyu sun kai ga karfafa fahimtar juna da amincewa da juna, hakan kuma ya shaida cewa, yin shawarwari da juna ya fi yin gaba da juna, kuma Sin da Amurka suna iya raya kansu tare da tabbatar da ci gabansu na bai daya.
Kasancewarsu kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, alhakin da ke rataya a wuyan Sin da Amurka ne su gano hanyar da ta dace ta cudanya da juna. Kasashen biyu za su iya karfafa ginshikin huldarsu da samar da kyakkyawan yanayi na bunkasa kansu, tare da samar da karin tabbas da kwarin gwiwa ga duniya, muddin sun tabbatar da daidaiton da shugabanninsu suka cimma, kuma suka yi hangen nesa tare da nacewa ga yin shawarwari da juna wajen daidaita sabaninsu, da kuma inganta hadin gwiwarsu da mu’amala da juna a kai a kai.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA