Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Sake Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Sansanin Falasdinawa Na Jabaliya
Published: 18th, April 2025 GMT
Sojojin mamayar Isra’ila sun sake aiwatar da wani sabon kisan kiyashi kan Falasdinawa 5 a sansanin Jabaliya da ke arewacin Gaza
Fararen hula 5 da suka hada da yara biyu da mace daya ne suka yi shahada, wasu kuma suka bace sakamakon harin da rundunar sojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gida a sansanin ‘yan gudun hijira na Tal al-Za’atar da ke gabashin Jabaliya da ke arewacin Zirin Gaza.
A cewar majiyoyin yankin, gidan da aka kai harin na dangin Nasiyo ne, kuma yana dauke da ‘yan gudun hijira daga iyalai sama da biyar a cikinsa, inda harin ya turbude su a karkashin baraguzan gine-gine.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
Kafofin yada labarai na kasa da kasa na matukar zura ido kan taron farko na tsarin tattaunawa game da tattalin arziki da cinikayyar Sin da Amurka da aka gudanar tsakanin ranekun 9 zuwa 10 ga watan nan da muke ciki a London na kasar Burtaniya.
An yi muhimmin shawarwarin ne kan matsaya daya bisa manyan tsare-tsaren da shugabannin kasashen biyu suka cimma a ran 5 ga watan nan. A wadannan raneku 2, wakilan Sin da Amurka sun yi mu’ammala mai zurfi cikin sahihanci, kuma sun amince da tabbatar da matsaya daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma ta wayar tarho da ba da tabbaci kan ci gaban da aka samu a yayin tattaunawar ciniki da tattalin arziki da aka gudanar a watan Mayun da ya gabata a Geneva.
Ban da wannan kuma, kasashen biyu sun samu sabon ci gaba kan batutuwan ciniki da tattalin arziki da suka tasa a gaba. Kazalika, bangarorin biyu sun nace ga bin hanya iri daya da tabbatar da matsaya daya da suka cimma.
A ganin wani farfesa na kwalejin koyar da ilmin diflomasiyya ta kasar Sin Li Haidong, tsarin tattaunawa da kasashen biyu suka cimma na bayyana niyyarsu ta tabbatar da huldarsu yadda ya kamata, kuma zai daidaita bambancin ra’ayinsu a sabon mataki da ma warware batutuwan ciniki da tattalin arziki da suka tasa a gaba, kana da ingiza bunkasa huldarsu a wannan bangare cikin kwanciyar hankali. A sa’i daya kuma, ci gaban da suka samu na biyan bukatun al’ummun duniya, tare da bayar da ingantaccen karfin raya tattalin arzikin duniya baki daya. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp