Leadership News Hausa:
2025-11-14@16:27:26 GMT

Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai

Published: 13th, April 2025 GMT

Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai

Newcastle ta lallasa Leicester da ci 3-0 a ranar Litinin a gasar Firimiya Lig ta Kasar Ingila, wasan wanda ya kasance na 8 a jere da Leicester City ta buga ba tareda jefa kwallo a raga ba, Newcastle da Eddie Howe ke jagoranta na fatan ganin sun samu gurbi a gasar Zakarun Turai na badi, tun da farko dai sun lashe gasar League Cup a watan da ya gabata.

Yanzu haka su na matsayi na biyar a kan teburin Firimiya, inda suke da maki daya da Chelsea da ta ke matsayi na hudu, Leicester City kuma a nata bangaren ka iya komawa gasar ‘yan dagaji ta Championship idan aka doke su a wasansu na gaba a gasar.

Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar Kaya

Newcastle, wacce arzikinta ya bunkasa tun bayan da mamallakanta ‘yan Kasar Saudiyya su ka karbi iko a shekarar 2021, ta na neman sake samun damar buga gasar Zakarun Turai tun bayan wanda aka kore ta a shekarar 2023/24 bayan shafe shekaru ashirin.

Howe, wanda ya jagoranci Newcastle lashe babban kofi na farko cikin shekaru 56 a wasan da su ka doke Liverpool a Wembley a watan da ya gabata, ya na da damar kara haskakawa a wannan kakar wasanni ta bana mai dimbin tarihi a wajen Newcastle.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗalibar BUK ta samu kyautar motar N35m a gasar MTN

Ɗalibar Aji uku a Sashen Nazarin Harkar Noma na Jami’ar Bayero ta Kano, Ramatu Yakubu, ta samu kyautar mota wadda kuɗinta ya kai Naira miliyan 35 a gasar da kamfanin MTN ya shirya a jami’ar.

Gasar wadda aka shafe kwanaki uku ana yi mai taken MTN “GoMAD on Campus,” wadda aka tsara domin tallafawa da nishaɗantar da ɗalibai ta hanyar wasanni, fasahar zamani da sauransu.

Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030

Ramatu ta lashe manyan kyaututtuka bayan shiga gasa daban-daban, inda sauran ɗalibai ma suka samu kyautar kwamfuta, wayoyi da kuɗi.

Manajan Sashen Matasa na MTN a Najeriya, Femi Adesina, ya ce kamfanin na son tallafa wa matasa da ke karatu a manyan makarantu.

“Mun yadda da matasan Najeriya. Ba wai magana kawai muke ba, muna tare da su, muna goyon bayansu domin su zama nagartattu,” in ji shi.

Taron da aka yi a Kano ya ƙunshi rawa da waƙoƙi, wasannin kwamfuta da sauransu.

MTN ya kuma bai wa ɗalibai ’yan kasuwa 10 dandalin nuna kayayyakinsu ba tare da biyan kuɗi ba.

Ɗalibai sun bayyana taron a matsayin ɗaya daga cikin abubuwan da suka faranta musu rai a jami’ar, inda suka gode wa MTN saboda tallafin da suka samu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗalibar BUK ta samu kyautar motar N35m a gasar MTN
  • Ɗalibar BUK ta samu motar N35m a gasar MTN
  • Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
  • Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana
  • Nijeriya ta doke Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • An kama mutum 3 kan zargin safarar yara 17 a Zariya
  • Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar Kano
  • Super Falconets ta lashe gasar WAFU ta ’yan ƙasa da shekaru 20
  • Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — Ronaldo
  • Bayan Da Muka Fara Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa