Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
Published: 13th, April 2025 GMT
Newcastle ta lallasa Leicester da ci 3-0 a ranar Litinin a gasar Firimiya Lig ta Kasar Ingila, wasan wanda ya kasance na 8 a jere da Leicester City ta buga ba tareda jefa kwallo a raga ba, Newcastle da Eddie Howe ke jagoranta na fatan ganin sun samu gurbi a gasar Zakarun Turai na badi, tun da farko dai sun lashe gasar League Cup a watan da ya gabata.
Yanzu haka su na matsayi na biyar a kan teburin Firimiya, inda suke da maki daya da Chelsea da ta ke matsayi na hudu, Leicester City kuma a nata bangaren ka iya komawa gasar ‘yan dagaji ta Championship idan aka doke su a wasansu na gaba a gasar.
Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar KayaNewcastle, wacce arzikinta ya bunkasa tun bayan da mamallakanta ‘yan Kasar Saudiyya su ka karbi iko a shekarar 2021, ta na neman sake samun damar buga gasar Zakarun Turai tun bayan wanda aka kore ta a shekarar 2023/24 bayan shafe shekaru ashirin.
Howe, wanda ya jagoranci Newcastle lashe babban kofi na farko cikin shekaru 56 a wasan da su ka doke Liverpool a Wembley a watan da ya gabata, ya na da damar kara haskakawa a wannan kakar wasanni ta bana mai dimbin tarihi a wajen Newcastle.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai
এছাড়াও পড়ুন:
Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
Fitaccen malamin Musulunci, Sheikh Ahmad Mahmud Abubakar Gumi, ya yi zargin cewa ƙasashen waje na taimaka wa ƙungiyoyin ’yan ta’adda Najeriya.
Sheikh Ahmad Gumi ya danganta ƙaruwar matsalar tsaro a Najeriya a baya-bayan nan da irin maganganun da ƙasashen waje suka riƙa yi a kai.
A yayin wata hira da BBC Hausa, malamin ya bayyana cewa yanayin taɓarɓarewar tsaro a baya-bayan nan ya nuna akwai alamun hannun ƙasashen waje a ciki.
Tsohon hafsan sojin, ya ce matsalar tsaro ta ragu a sassan ƙasar nan sai baya-bayan nan da ƙasashen waje suka fara magana a kai.
Ya bayyana cewa an samu aminci a hanyar Abuja zuwa Kaduna, wadda baya ta kasance tarkon mutuwa, amma sai kwanan nan matsalar ta fara dawowa bayan maganganun ƙasashen waje.
Ya ce manoma a yankin Birnin Gwari sun ci gaba harkokin nomansu, bayan samuwar zaman lafiya, abin da ya gare su a baya lokacin da ake ganiyar rashin tsaro.
“Akwai maganar da ƙasashen waje suka yi, kuma mun jima muna cewa ƙasashen waje ke taimak aa ’yan ta’adda da irin muggan makamai da suke amfani da su.
“Akwai attajirai da shugabannin ƙasashen waje da ke yin katsalandan ga harkokin wasu ƙasashe.”
Don haka ya ce ba abin mamaki ba ne samun ƙaruwar hare-haren ta’addanci da aka yi a Najeriya bayan maganganun ƙasashen waje a kan matsalar tsaro a ƙasar.
Kan matsayinsa game da tattaunawa da ’yan bindiga, ya ce: “Kowa ya san su. Amma abin da mutane ba sa magana a kai shi ne: me ya sa mutanen da muka taɓa rayuwa lafiya da su suka juya mana baya suka zama annoba a cikin al’umma? Akwai dalili.”
“Mutane biyu ne ba za a yi mamakin abin da suke yi ba: mahaukaci da jahili. Babu wani bayani da za ka yi musu da zai sa su fahimci cewa aikata laifi ba daidai ba ne.”
“Babu abin da suka sani face ɓarna. Amma wa zai yi musu nasiha su daina? Lokacin da muka yi ƙoƙarin kusantar su muka gaya musu cewa haramun ne sata, ƙwace dukiyar mutane haramun ne, yin garkuwa da mutane haramun ne, gwamnatin da ta gabata ba ta ba mu goyon baya ba.
“Da an ba da wannan goyon bayan, watakila da zuwa yanzu an warware wannan matsala.”
Sheikh Gumi ya yi gargaɗi cewa muddin ba a magance tushen matsalar ba, to akwai sauran rina a kaba.
Ya kuma ja hankali jama’a su fahimci cewa matakin yaki da ta’addanci da ya ɗauka, musamman neman sulhu da ’yan bindiga ba, ba ya nufin goyon bayan ayyukansu.
“Addininmu ya haramta zalunci; Duk abin da muke yi, muna yi ne domin Allah,” in ji shi.