Jami’an tsaro Gwamnatin Tarayya suna sassauta wa masu kashe mutane babu gaira babu dalili a Jihar Filato, a cewar tsohon jihar na mulkin soji, Rear Admiral Samuel Bitrus Atukum.

Da yake tsokaci kan kisan gillar da ka yi wa mutane 52 tare da lalata kadarori na miliyoyin naira baya-bayan nan a yankin Ƙaramar Hukumar Bokkos, Atukum ya ce, “Ina da matsala kan yadda jami’an tsaro ke tunkarar matsalar.

A gani na suna sassauta musu. Mene ne abu mai wahala a ba wa sojoji umarni su je maɓoyar masu wannan aika-aika su kamo su?

“Daga kan tsaunuka mutanen nan suke saukowa ɗauke da makamai su halaka jama’a, sannan su ɓace, kuma a nan suke ɓoye makamansu. Saboda haka ya kamata jami’an tsaro su yi fiye da  abin da suke yi yanzu.

“Kamata ya yi a ayyana waɗannan mutane a matsayin ’yan ta’adda, saboda ta’addanci suke yi, amma an kasa, sai a je ana kama masu ƙananan laifi da sunan manyan laifuka,” in ji Atukum wanda shi ne gwamnan Filato daga 1984 zuwa 1985.

Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato Mutane 300 sun kamu da cutar sanƙarau Sakkwato

Ya bayyana cewa a lokacin da yake gwamna rikicin addini na ƙungiyar Maitatsine ya ɓarke, amma cikin ɗan ƙanƙanin lokaci aka murƙushe shi, saboda gwamnati ta tari matsalar tun daga tushe kafin a je ko’ina.

Ya ce idan za a ɗauki irin matakin daga sama a kan matsalar tsaron Filato, shugaban ƙasa ya ba wa jami’an tsaro umarni a matsayinsa na Babban Kwamandan Tsaron Ƙasa, za su yi abin da ya kamata.

“Amma ba a ba da umarni ko ɗaukar mataki ba, sai mutane sun yi ta ƙorafi kan matakin da gwamnati ta ɗauka, sai a fito ana cewa za a kamo waɗanda suka aikata abin, a hukunta su daidai da abin da doka ta tanada. Wannan shi ne abin da muke ta ji.”

Ya ce, “Da ni ke da iko, da umarni da wa’adi ƙarara zan na wa jami’an tsaro cewa ga abin da nake so. Idan shugaban ƙasa da gaske yake kan matsalar tsaro, umarni kawai zai bayar kuma yana da tasiri a kan Majalisar Dokoki ta Ƙasa, duk abin da yake so za ta yi aiki a kai, kuma a tafi tare da ɗaukacin al’ummar ƙasa.

“Amma ya za a yi ka ce kana maganin abun, amma ba a ga alamar komai ba? Wa zai ɗauka da gaske kake, alhali ba a ga an kamo masu aikata laifin an hukunta su ba?

“A wannan yanayi da matsala ke fama da matsalar rashin aiki, mutane za su yi ta amfani da irin wannan giɓi wajen yin irin waɗannan aika-aika da muke gani.

“Har ta kai ga masu yin wannan ta’asa na ba da umarnin cewa ga wanda suke so a naɗa a matsayin shugaɓan wata hukumar tsaro, ko kuma a sauke wanda yake kai,” in ji tsohon gwamnan sojin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hukumomin tsaro Jami an Tsaro jami an tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure