Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum
Published: 8th, April 2025 GMT
Gwamnan Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayyana damuwa kan hare-haren da kungiyar ‘yan ta’addan Boko Haram suke kai wa manyan sojoji a baya-bayan nan.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da yake jagorantar taron kwamitin tsaro da aka gudanar a zauren majalisar, gidan gwamnati, Maiduguri, yana mai cewa jihar na fuskantar barazanar komawa cikin tashin hankali.
“An gurgunta matsugunan soji da dama musamman a garuruwan Wulgo, Sabongari, Wajirko da sauransu. Alamu na nuna ‘yan ta’adda sun fara nasara akanmu. Don haka wannan abu ne mai matuƙar muhimmanci da muke buƙatar tattaunawa.
“Daga shekaru uku baya zuwa yanzu a hankali zaman lafiya ya fara dawowa Borno, amma lamarin ya sauya a ‘yan kwanakin nan,” in ji shi
Zulum ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tura jiragen yaƙi masu saukar ungulu, da sabbin jirage marasa matuka da aka saya domin tallafawa ayyukan soja a wuraren da abin ya shafa.
“Duk da muna yaba wa sojojin Najeriya, ‘yan sanda, da jami’an DSS kan kiyaye doka da oda a Borno, dole ne mu kuma faɗi gaskiya, in ba haka ba, duk nasarorin da muka samu ya zuwa yanzu za su zama na banza,” in ji shi
Gwamnan, wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jajirce waje. Tabbatar da yankin arewa maso gabashin kasar ya samu kulawar da ta kamata.
“Hankalin sojojin Najeriya da ma’aikatar tsaro ba akan jihohin arewa maso gabas yake ba, la’akari da halin da yankin ke ciki, mun cancanci samun kulawar da muke kira a ba mu.
“Yankin Sahel yana da matukar muhimmanci, kuma Borno ta yi iyaka da Jamhuriyar Chadi, Nijar da Kamaru.
“Yawancin ‘yan kasashen na shigowa Najeriya ne ta Borno, don haka idan ba a yi abinda ya kamata ba, jihar za ta sake shiga cikin rikici.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: matsalar tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’uSauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.
An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.
Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.
Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.
Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.