Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum
Published: 8th, April 2025 GMT
Gwamnan Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayyana damuwa kan hare-haren da kungiyar ‘yan ta’addan Boko Haram suke kai wa manyan sojoji a baya-bayan nan.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da yake jagorantar taron kwamitin tsaro da aka gudanar a zauren majalisar, gidan gwamnati, Maiduguri, yana mai cewa jihar na fuskantar barazanar komawa cikin tashin hankali.
“An gurgunta matsugunan soji da dama musamman a garuruwan Wulgo, Sabongari, Wajirko da sauransu. Alamu na nuna ‘yan ta’adda sun fara nasara akanmu. Don haka wannan abu ne mai matuƙar muhimmanci da muke buƙatar tattaunawa.
“Daga shekaru uku baya zuwa yanzu a hankali zaman lafiya ya fara dawowa Borno, amma lamarin ya sauya a ‘yan kwanakin nan,” in ji shi
Zulum ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tura jiragen yaƙi masu saukar ungulu, da sabbin jirage marasa matuka da aka saya domin tallafawa ayyukan soja a wuraren da abin ya shafa.
“Duk da muna yaba wa sojojin Najeriya, ‘yan sanda, da jami’an DSS kan kiyaye doka da oda a Borno, dole ne mu kuma faɗi gaskiya, in ba haka ba, duk nasarorin da muka samu ya zuwa yanzu za su zama na banza,” in ji shi
Gwamnan, wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jajirce waje. Tabbatar da yankin arewa maso gabashin kasar ya samu kulawar da ta kamata.
“Hankalin sojojin Najeriya da ma’aikatar tsaro ba akan jihohin arewa maso gabas yake ba, la’akari da halin da yankin ke ciki, mun cancanci samun kulawar da muke kira a ba mu.
“Yankin Sahel yana da matukar muhimmanci, kuma Borno ta yi iyaka da Jamhuriyar Chadi, Nijar da Kamaru.
“Yawancin ‘yan kasashen na shigowa Najeriya ne ta Borno, don haka idan ba a yi abinda ya kamata ba, jihar za ta sake shiga cikin rikici.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: matsalar tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
Kwanaki takwas bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar Ƙaramar hukumar Mokwa a Jihar Neja, an gano gawar mutum ɗaya daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, an tsinci gawar ne a ranar Alhamis a wata gona da ke kan hanyar wucewa kusa da wani wuri da aka fi sani da ‘dam’.
Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiA cewar shaidun gani da ido, an kasa tantance wanda abin ya shafa saboda gawar ta lalace. An binne shi ne a inda aka gano gawarsa.
Wata mazauniyar yankin mai suna Tswata Mai Rubutu da ta zanta da Aminiya ta wayar tarho, ta ce an tsinci gawar a kan hanyar da ruwa ke wucewa.
“Gawar wani babban mutum ne, amma ba za mu iya gane shi ba saboda tuni ya fara lalacewa. An binne shi a wurin tun da ba a iya motsa gawar,” in ji shi.
An yi ƙoƙarin jin ta bakin Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, domin ƙarin bayani lamarin ya ci tura.
Tun da farko hukumar ta tabbatar da mutuwar mutane 161, yayin da wasu da dama suka ɓace bayan iftila’in ambaliyar.