Gobara ta kona motoci 10 a garejin Borno Express
Published: 8th, April 2025 GMT
Wata gobara da ta ɓarke ta cinye garejin gyaran motocin kamfanin sufurin Borno Express na Gwamnatin Jihar Borno, inda ta lalata motocin bas sama da 10 masu daukar mutane 18 kowacce.
Shaidu sun ce gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 12 na rana a ranar Litinin, bayan wani fashewa mai ƙarfi a harabar garejin.
Ko da yake babu wanda ya rasa ransa a wannan lamarin, wani ma’aikacin hukumar kashe gobara ya samu raunuka yayin da yake kokarin kashe gobarar.
Wani ganau ya ce, “Gobarar ta tashi ne sakamakon fashewar tukunyar gas — inda wani kara mai ban tsoro ya sa ma’aikata da matafiya a yankin suka yi ta gujegujen domin tsira.”
Gobara ta laƙume ƙauyuka a Borno Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga MayuYa ƙara da cewa, “Hanzarin da hukumar kashe gobara ta yi ne ya hana lamarin ƙara ƙazancewa. Sun isa da sauri kuma sun yi nasarar shawo kan gobarar.”
Kwamishinan Sufuri da Makamashi na Jihar Borno, Aliyu Buba Bamanga, ya ziyarci wurin da lamarin ya faru amma ya ƙi yin tsokaci.
Kwamishinan ya ce, “Muna jiran Mai Girma Gwamna Babagana Umara Zulum nan ba da jimawa ba. Ba zan so yin magana kafin wata sanarwa ta hukuma daga gare shi ba.”
Wani ma’aikacin garejin ya shaida wa wakilinmu cewa galibin motocin da abin ya shafa motocin bas ne masu ɗaukar mutane 18 da ake yi wa gyaran yau da kullum, da kuma wasu ƙalilan da ake yi musu manyan gyare-gyare.
“Mun auna arziki da gobarar ba ta shafi wurin cajin motocin lantarki da ke kusa ba, da gobarar ta kai can, da munin lamarin ya ɓaci.”
Garejin gyaran motocin, wanda Kamfanin Sufuri na Borno Express ke gudanarwa, yana da alhakin kula da motocin zirga-zirgar jama’a na jihar.
Wannan lamarin ya faru ne kwana daya kacal bayan wata gobara ta cinye dubban gidaje a wasu yankuna huɗu a Alau, Jihar Borno, ind ta yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu tare da lalata dukiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.