Gobara ta kona motoci 10 a garejin Borno Express
Published: 8th, April 2025 GMT
Wata gobara da ta ɓarke ta cinye garejin gyaran motocin kamfanin sufurin Borno Express na Gwamnatin Jihar Borno, inda ta lalata motocin bas sama da 10 masu daukar mutane 18 kowacce.
Shaidu sun ce gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 12 na rana a ranar Litinin, bayan wani fashewa mai ƙarfi a harabar garejin.
Ko da yake babu wanda ya rasa ransa a wannan lamarin, wani ma’aikacin hukumar kashe gobara ya samu raunuka yayin da yake kokarin kashe gobarar.
Wani ganau ya ce, “Gobarar ta tashi ne sakamakon fashewar tukunyar gas — inda wani kara mai ban tsoro ya sa ma’aikata da matafiya a yankin suka yi ta gujegujen domin tsira.”
Gobara ta laƙume ƙauyuka a Borno Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga MayuYa ƙara da cewa, “Hanzarin da hukumar kashe gobara ta yi ne ya hana lamarin ƙara ƙazancewa. Sun isa da sauri kuma sun yi nasarar shawo kan gobarar.”
Kwamishinan Sufuri da Makamashi na Jihar Borno, Aliyu Buba Bamanga, ya ziyarci wurin da lamarin ya faru amma ya ƙi yin tsokaci.
Kwamishinan ya ce, “Muna jiran Mai Girma Gwamna Babagana Umara Zulum nan ba da jimawa ba. Ba zan so yin magana kafin wata sanarwa ta hukuma daga gare shi ba.”
Wani ma’aikacin garejin ya shaida wa wakilinmu cewa galibin motocin da abin ya shafa motocin bas ne masu ɗaukar mutane 18 da ake yi wa gyaran yau da kullum, da kuma wasu ƙalilan da ake yi musu manyan gyare-gyare.
“Mun auna arziki da gobarar ba ta shafi wurin cajin motocin lantarki da ke kusa ba, da gobarar ta kai can, da munin lamarin ya ɓaci.”
Garejin gyaran motocin, wanda Kamfanin Sufuri na Borno Express ke gudanarwa, yana da alhakin kula da motocin zirga-zirgar jama’a na jihar.
Wannan lamarin ya faru ne kwana daya kacal bayan wata gobara ta cinye dubban gidaje a wasu yankuna huɗu a Alau, Jihar Borno, ind ta yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu tare da lalata dukiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara
এছাড়াও পড়ুন:
Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
Akalla mutane 7 ne aka ceto, bayan kifewar kwale-kwale a wani kogi da ke Zangon Maje, ƙaramar hukumar Taura, ta jihar Jigawa ranar Litinin.
Shugaban ƙaramar hukumar Taura, Dr Shuaibu Hambali ne ya bayyana hakan ga Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.
A cewarsa, lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, lokacin da wasu manoma ke dawowa daga gonakinsu a ƙauyen Zangon Maje, inda suka hau kwale-kwalen.
Ya ce, jami’an bada agajin gaggawa na yankin sun samu nasarar ceto mutane 7 a kokarin da suka yi na ceto wadanda lamarin ya shafa.
Ya ƙara da cewa, masu ceton sun gano gawar mutum guda a yankin Yalleman da ke ƙaramar hukumar Kaugama.
Dr Shuaibu ya bayyana cewa, sauran mutane 9 da ke cikin jirgin har yanzu ba a same su ba a lokacin da ake bayar da wannan rahoto.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, ba a fitar da sunayen waɗanda abin ya shafa ba, amma lamarin ya jefa al’ummar yankin cikin jimami da baƙin ciki.
Shugaban ƙaramar hukumar ya bayyana cewa, za a raba rigunan kariya (life jacket) ga fasinjoji a nan gaba kadan domin kiyaye sake afkuwar lamarin nan gaba.
Ya kuma gargadi matuka kwale-kwale da su kiyaye ƙa’idojin tsaro da kaucewa cunkoson fasinjoji, musamman da yamma a lokacin damina, inda ruwa ke ƙaruwa a kowane lokaci.
Dr Hambali, wanda ya isa wurin da abin ya faru, ya jajanta wa iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Wasu daga cikin mazauna yankin da Rediyon Najeriya ta tattauna da su, sun nemi gwamnatin ta gaggauta ɗaukar matakan da suka dace, tare da inganta hanyoyin sufuri ta ruwa.
Usman Muhammad Zaria