Haka kuma, an gargaɗi kamfanonin da ke da alhakin kawo mutane Umrah cewa idan suka ƙi bayyana sunayen waɗanda suka ƙi dawowa gida, za a ci su tara har riyal 100,000.

Ma’aikatar ta buƙaci kowa ya bi doka domin guje wa hukunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Saudiyya Umrah

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar

Shugaban kwamitin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya ce kwamatin ya jinkirta rangadin kananan hukumomin jihar 27 a Zango na uku na shekarar 2024 ne a sakamakon zaben kananan hukumomi, don haka akwai bukatar ba su damar gudanar da ayyuka kafin tantance kwazon su.

 

Alhaji Aminu Zakari ya yi wannan tsokaci ne a sakatariyar karamar hukumar Sule Tankarkar a ci gaba da rangadin kananan hukumomi da kwamatin yake yi.

 

A cewar sa, kwamatin zai tantance kasafin kudin karamar hukumar na shekarar 2024 da 2025 na ayyuka ta da jerin ayyukan raya kasa, da  takardun biyan kudaden ayyukan da littafin ta’ammalin kudaden na banki.

 

Yace kwamitin zai tantance takardun kudaden shiga tare da duba kudin tarukan bangaren zartaswa da na kansiloli domin tabbatar da bin ka’idojin kashe kudaden gwamnati.

 

Karamin kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya ya duba aikin masallacin kamsissalawati na Rugar Danqulili, da famfunan tuka tuka a Gabala/Dangwanki da Yanyawai da Fulanin Tagai da Rugar Hardo Daudu da gidan ungozoma a asibitin Jeke, da shirin noman rani a Maitsamiya.

 

Kazalika, kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya duba aikin gidan ruwa mai amfani da hasken rana a unguwar Sule Gabas da masallacin Juma’a na Hammado da makarantar Tsangaya a Danladi, da masallaci kamsissalawati na gidan mulki na Shugaban karamar hukumar da famfon tuka tuka na Gidan Idi Ruwa.

 

A nasa Jawabin, Shugaban karamar hukumar Sule Tankarkar Malam Tasi’u Adamu, Ya lura cewar, tantance sha’anin mulki da harkokin kudin kananan hukumomi ko shakka babu zai taimaka wajen kawo ci gaban yankunan karkara.

 

Malam Tasi’u Adamu ya kuma yi addu’ar samun nasarar ziyarar kwamatin domin ta yi tasiri wajen kawo cigaban rayuwar jama’ar yankin.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati