Aminiya:
2025-11-03@04:26:09 GMT

Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato

Published: 8th, April 2025 GMT

Gwamnatin Sakkwato ta yi barazanar sanya ƙafar wando da waɗanda ta yi zargi suna ƙoƙarin kawo mata cikas a yaƙin da take yi da ’yan bindiga da sauran matsalolin tsaro a Jihar.

Ta gargaɗi mazauna da su shiga taitayinsu game da yin kalamai da za su iya kawo cikas ga ƙoƙarinta na magance matsalar rashin tsaro a jihar.

Wannan gargaɗin ya biyo bayan wata sanarwa da ake dangantawa wani mai suna Basharu Altine Guyawa wanda ya yi ƙoƙarin nuna cewa gwamnati ba ta yi abin da ya kamata ba a fannin tsaro.

Mai ba Gwamna Ahmed Aliyu shawara na musamman kan harkokin tsaro, Kanar Ahmed Usman mai ritaya, ya yi wannan gargaɗin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu

Usman ya ce irin wannan kalaman suna iya sanya mutane butulce wa abin da gwamnati da jami’an tsaro suke yi wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro a jihar.

Ya ce “Ya kamata mutanenmu su guji yin magana da tayar da hankali da kuma siyasantar da matsalar tsaro. A maimakon haka, ya kamata su goyi bayan gwamnati a ƙoƙarinta na neman hanyoyin magance matsalolin tsaronmu na dindindin.

“Gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunƙurin wani mutum ko ƙungiya na kawo cikas ga ƙoƙarinta ko kuma shagaltar da ita a wannan batun ba.

“Gwamnatin jihar tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro sun kasance suna aiki tuƙuru don maido da zaman lafiya, musamman a yankin gabashin jihar da ke fuskantar ƙalubalen tsaro.

“Gwamnati kwanan nan ta yi wani aiki na haɗin gwiwa a yankin wanda ya samu gagarumar nasara yayin da aka lalata maboyar ’yan bindiga da dama da aka gano tare da kashe ’yan ta’adda da dama a cikin aikin. Bugu da ƙari, an kuma ceto daruruwan waɗanda aka yi garkuwa da su a lokacin aikin.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargaɗi Sakkwato Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Taron kaddamar da rabar da taraktocin noman, ya gudana ne a Shalkwatar Ma’aikatar Kula da Aikin noma da kuma yin Noman Rani da ke garin Kalaba.

 

Kazalika, taron ya samu halartar ‘yan Majalisa da Sarakunan Gargajiya da kungiyoyin manoma mata da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma da ke jihar da abokan hadaka.

 

Daukacinsu, sun jinjina wa wannan kokari na gwamna Bassey, kan wannan hangen nesa da gwamnatinsa ta yi, na kaddamar da taraktocin noman, musamman domin ciyar da fannin aikin noman jihar gaba, duba da cewa; fannin ne kinshikin tattalin arzikin jihar.

 

Har ila yau, gwamna Bassey, ya nanata kudurin gwamnatinsa wajen ci gaba da bai wa fannin aikin noma muhimmanci a matsayin fannin da ke kara habaka tattalin arzikin jihar.

 

“A lokacin da na karbi jan ragamar shugabancin jihar, mun samar da dabaru da kuma daukar matakai daban-daban, domin kara habaka fannin,“ in ji gwamna Bassey.

 

“Biyo bayan wata ganawa da muka yi da manoman da ke daukacin kananan hukumominmu, mun gano cewa; kalubalen da suke fuskanta sama da kashi 70 cikin dari, na shiye-shiyen share gonakansu ne, domin fara noma su; saboda kudaden da suke kashewa masu yawa, wajen gyaran gonakin nasu, muna da yakinin wannan shirin zai magance wadannan matsaloi,” a cewar gwamnan.

 

Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; wannan rabar da taraktocin noma, wadanda ba sa shan man sosai, an tsara su ne kan yadda manoma za su yi gyaran gonakinsu cikin sauki tare kuma da rage musu kashe kudade masu yawa da kuma kara habaka fannin na aikin noma.

 

“Kashi 108 na kashin farko na shirin, an raba wa manoman jihar jimillar taraktocin noma 324, wadanda kuma aka rabar da su a daukacin fadin jihar,“ a cewar gwamnan.

 

Gwamna Bassey ya ci gaba da cewa, za a ci gaba da kula da taraktocin ne a karkashin tsarin kungiyoyin manoma na jihar.

 

“Hakan zai bai wa wadanda suka amfana da taraktocin damar daukar nauyin ci gaba da kula da su, wanda kuma sauran manoman da ke karkara a jihar, su ma za su samu damar samun taraktocin,” in ji shi.

 

“Ta wannan hanyar, za mu samu damar cin gajiyar da ke fannin noma na jihar, wanda hakan zai kuma bai wa manoman jihar kara dagewa, domin yin noma da samun kudaden shiga da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar,” a cewar tasa.

 

Kazalika, gwamnan ya kuma zayyano wasu ayyukan noma da gwamnatinsa ta kaddamar da su da suka hada da na samar da Irin noman Rogo, aikin noman Masara da na Waken Soya da sauransu.

 

Ya bayyana cewa, gwamnatin na kuma ci gaba da habaka samar da Irin Farin Wake da rabar da kayan aikin noma ga kananan manoma tare da kuma shirye-shiyen noman Koko (Cocoa) da Ganyen Shayi, wanda za gudanar ta hanyar yin hadaka da gwamnatin da kuma ‘yan kasuwa.

 

“Kaddamar da rabar da wadannan taraktocin noman, na daya daga cikin kason farko na kudurin gwamnatinmu na bunkasa fannin aikin noma na jihar, musamman ta hanyar yin amfani da kayan aikin noma na zamani,” in ji gwamnan.

 

Shi ma, shugaban kamfanin da ya yi kwangilar kawo taraktocin, Femi Odeshirin, ya yaba wa shirin, wanda ya ce; hakan zai kara bunkasa fannin aikin noma na jihar.

 

“Ba wai kawai rabar da wadannan taraktocin noma ga manoman jihar ba ne da gwamnan ya yi ba, hakan zai kuma kara inganta rayuwar manoman da suka amfana,” in ji Odeleye.

 

Ya bayyana cewa, kamfanin na kuma kan shirin kafa masana’antar da ake hada taraktocin noma a garin Kalaba da ke jihar, inda masana’antar za ta samar da ayyukan yi sama da 2,000.

 

Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa (AFAN) reshen jihar, Ojikpong Nyiam Bisong, danganta salon shugabancin gwamna Bassey ya yi da na marigayi tsohon Firimiyan Kudancin Nijeriya, Dakta Michael Okpara.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya October 18, 2025 Noma Da Kiwo Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul October 18, 2025 Noma Da Kiwo Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI October 18, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari