Leadership News Hausa:
2025-05-01@00:10:59 GMT

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 4, Sun Sace 45 A Katsina

Published: 8th, April 2025 GMT

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 4, Sun Sace 45 A Katsina

A ƙauyen Maikuma, da ke cikin ƙaramar hukumar Dandume ta Jihar Katsina, ana zargin wasu ƴan bindiga sun kashe mutane 4 sannan suka sace a ƙalla 45. Harin ya faru ne a daren Lahadi, lokacin da wata babbar tawagar ‘yan fashin ɗauke da makamai ta kai farmaki a cikin al’umma.

Shaidu sun bayyana cewa masu farmakin sun shige gidaje daga a jere a jere suna aiki har tsawon awanni kafin su gudu zuwa dajin da ke kusa da su tare da waɗanda suka sace.

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10, Sun Ceto Mutane 101 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara. ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kwamandan ‘Yan Sa-kai, Sun Jikkata Wasu A Katsina

Duk da ƙoƙarin jami’an tsaro, ba su samu nasarar bin ƴan bindigar ba zuwa bayan iyakar garin. Shugaban ƙaramar hukumar Dandume, Basiru Musa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa adadin masu farmakin sun kai fiye da 100.

Musa ya nuna damuwa game da yadda hare-haren ke faruwa akai-akai, yana kira ga hukumomi su ƙara tsaurara matakan tsaro don kare al’ummomin da ke cikin hatsari. Hukumomin tsaro na Jihar Katsina har kawo yanzu ba su fitar da wata sanarwa ta hukuma ba game da lamarin ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Terrorist

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ci gaba da killace Gaza da kuma kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, laifi ne da ba a taba yin irinsa ba a tarihin dan Adam

A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Masar Badar Abdel Ati a yammacin jiya Lahadin da ta gabata, Araqchi ya bayyana ci gaba da killace yankin Gaza da rashin abinci da magunguna, tare da kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, a matsayin wani laifi da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin dan Adam. Ya dauki Amurka da sauran masu goyon bayan ‘yan sahayoniyya a matsayin masu hannu a kisan kiyashi da laifukan yaki da ake aikatawa a Gaza.

Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada wajibcin tunkarar muggan manufofin yahudawan sahayoniyya na tilastawa al’ummar Gaza da yammacin kogin Jordan yin hijira daga muhallinsu, yana mai bayyana halin ko in kula da kasashen duniya suke nun awa kan wadannan laifuka a matsayin abin mamaki da damuwa.

Araghchi ya kuma yi wa takwaransa na Masar bayani kan ci gaban tattaunawar Iran da Amurka kan Shirin makamashin nukiliya na zaman lafiya da ake takaddama a kai tsawon shekaru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara