HausaTv:
2025-04-30@18:57:28 GMT

Gaza : adadin ‘yan jaridar da aka kashe ya haura 210

Published: 7th, April 2025 GMT

Ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza ya bayyana cewa adadin ma’aikatan yada labarai da aka kashe a hare-haren da Isra’ila ke kaiwa Zirin tun daga watan Oktoban 2023 ya kai 210 bayan kashe dan jarida Helmi al-Faqawi.

Al-Faqawi na cikin akalla mutane biyu da suka mutu a lokacin da jiragen yakin Isra’ila suka kai hari kan wani tanti na ‘yan jarida kusa da wani asibiti a Khan Younis da sanyin safiyar ranar Litinin din nan.

Akalla mutane bakwai ne kuma suka jikkata a harin.

A cikin wani rahoto da aka buga a ranar 1 ga Afrilu, Cibiyar Watson ta ce yakin da Isra’ila ta yi a Gaza ya kasance mafi muni ga ma’aikatan yada labarai da aka yi rikodin kuma sojojin Isra’ila sun kashe ‘yan jarida 232 tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Hakan na nufin an kashe ‘yan jarida da yawa a Gaza fiye da yakin duniya na biyu, yakin Vietnam, yakin Yugoslavia da yakin Amurka a Afganistan.

A wani labarin kuma adadin wadanda suka mutu a Gaza tun soma yakin ya haura 50,700

Akalla mutane 57 ne aka kashe a Gaza a cikin sa’o’i 24 da suka gabata, yayin da 137 suka samu raunuka, kamar yadda ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza ya sanar.

Tun bayan da Isra’ila ta sake kai hare-hare a Gaza a ranar 18 ga Maris, adadin wadanda suka mutu ya kai 1,391, yayin da 3,434 suka jikkata.

Adadin wadanda aka kashe tun daga ranar 7 ga Oktoban 2023 yanzu ya kai 50,752 yayin da wadanda aka jikkata ya kai 115,475.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yada labarai

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar yankin Borno ta Kudu, ya bayyana cewa hare-haren na ƙara ƙamari a yankin abun takaici ne.

Ya ce ya samu rahoto tsakanin Hawul da Garkida inda aka ce an kashe ’yan sa-kai sama da 10 a ranar Litinin.

A cewarsa, sama da mutane 100 aka kashe cikin wata guda a hare-hare da aka kai Sabon Gari, Izge, Kirawa, Pulka, Damboa, Chibok, Askira Uba da wasu garuruwa da dama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa