Gaza : adadin ‘yan jaridar da aka kashe ya haura 210
Published: 7th, April 2025 GMT
Ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza ya bayyana cewa adadin ma’aikatan yada labarai da aka kashe a hare-haren da Isra’ila ke kaiwa Zirin tun daga watan Oktoban 2023 ya kai 210 bayan kashe dan jarida Helmi al-Faqawi.
Al-Faqawi na cikin akalla mutane biyu da suka mutu a lokacin da jiragen yakin Isra’ila suka kai hari kan wani tanti na ‘yan jarida kusa da wani asibiti a Khan Younis da sanyin safiyar ranar Litinin din nan.
Akalla mutane bakwai ne kuma suka jikkata a harin.
A cikin wani rahoto da aka buga a ranar 1 ga Afrilu, Cibiyar Watson ta ce yakin da Isra’ila ta yi a Gaza ya kasance mafi muni ga ma’aikatan yada labarai da aka yi rikodin kuma sojojin Isra’ila sun kashe ‘yan jarida 232 tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.
Hakan na nufin an kashe ‘yan jarida da yawa a Gaza fiye da yakin duniya na biyu, yakin Vietnam, yakin Yugoslavia da yakin Amurka a Afganistan.
A wani labarin kuma adadin wadanda suka mutu a Gaza tun soma yakin ya haura 50,700
Akalla mutane 57 ne aka kashe a Gaza a cikin sa’o’i 24 da suka gabata, yayin da 137 suka samu raunuka, kamar yadda ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza ya sanar.
Tun bayan da Isra’ila ta sake kai hare-hare a Gaza a ranar 18 ga Maris, adadin wadanda suka mutu ya kai 1,391, yayin da 3,434 suka jikkata.
Adadin wadanda aka kashe tun daga ranar 7 ga Oktoban 2023 yanzu ya kai 50,752 yayin da wadanda aka jikkata ya kai 115,475.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yada labarai
এছাড়াও পড়ুন:
Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
Falasdinawa 78 ne aka kashe a yau a Gaza, mafi yawansu a birnin Gaza a yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare a kasa da kuma umarnin tilastawa mazauna Gaza yin kaura.
An bayar da rahoton karin mutuwar mutane uku sakamakon yunwa da killace yankin.
Mazauna Gaza sun bayyana tashin bama-baman a matsayin abun tashin hankali da kuma yunkurin shafe wata al’umma.
Sojojin Isra’ila sun zafafa kai hare-hare a birnin Gaza, inda suka kai hari kan unguwannin da ke da yawan jama’a. Katangar da Isra’ila ta kakaba mata da kuma karancin abinci na ci gaba da zurfafa rikicin jin kai.
Yakin da Isra’ila ta kwashe watanni ana yi a Gaza ya janyo hasarar rayukan fararen hula da dama.
Tun daga watan Oktoban 2023, hare-haren sojojin Isra’ila a Gaza sun kashe a kalla Falasdinawa 64,964 tare da jikkata sama da 165,312, a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza. Yayin da ake fargabar wasu dubbai na karkashin baraguzan gine gine.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan September 16, 2025 Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci