Leadership News Hausa:
2025-11-02@17:17:25 GMT

Ya Kamata A Yi Adawa Da Kama Karya A Tabbatar Da Adalci

Published: 7th, April 2025 GMT

Ya Kamata A Yi Adawa Da Kama Karya A Tabbatar Da Adalci

Game da matakin Amurka na kakaba “harajin fito na ramuwar gayya”, kasar Sin ta gabatar da jerin matakai don mayar da martani, da kuma bayyana ra’ayin gwamnatin kasar na kin amincewa da sabon tsarin haraji na kasar Amurka. Cikin bayanin da Sin ta fitar a ranar 5 ga wannan wata, ta yi nuni da cewa, kasar Amurka ta yi amfani da haraji a matsayin makamin matsawa sauran kasashe lamba da neman samun moriya ita kadai, wanda mataki ne da aka dauka bisa ra’ayin bangare daya da ba da kariya ga cinikayya da cin zarafin tattalin arziki, kuma Sin ta jaddada cewa, ba ta jin tsoron tinkarar wannan batu, kuma za ta ci gaba da aiwatar da manufofin cinikayya masu inganci da zuba jari cikin ‘yanci da sauki, ta yadda za ta more damar samun bunkasuwa da moriyar juna tare da kasa da kasa a duniya.

Ta wannan bayani, ana iya gano ra’ayin Sin na kin amincewa da kama karya da neman tabbatar da adalci. Farfesa a kwalejin ilmin harkokin diplomasiyya na kasar Sin Li Haidong ya bayyana cewa, wannan bayani ya shaida cewa, kasar Sin ba ta tsoron ra’ayin kama karya, kuma tana son a tabbatar da adalci, da taimakawa kasa da kasa wajen yin hadin gwiwa da kokari tare don sa kaimi ga raya tattalin arziki bisa tsarin bai daya a duk duniya. Hakazalika kuma, kasar Sin ta ci gaba da sa kaimi ga bude kofa ga kasashen waje, da kara imanin sauran kasashe na kin amincewa da ra’ayin kama karya, da ba da tabbaci ga yanayin duniya dake canjawa.

Ya kamata a bi ka’idoji da adalci a fadin duniya. Samun bunkasuwa ‘yanci ne na dukkan kasashen duniya, ba na wasu kasashe kadai ba. Kasar Amurka ta kara buga harajin kwastam ga dukkan kasashe abokan cinikayya daga bangare daya, lamarin da ya sabawa ka’idojin dake shafar kasashen da aka fi ba su gatanci na WTO, da sabawa odar tattalin arziki da cinikayya ta duniya. Amurka tana son zama gaban komai kuma ta musamman, kana tana son kwace ‘yancin sauran kasashen duniya na samun ci gaba. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.

 

Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher