Kofin Duniya: Kocin Nijeriya Na Fatan Matashin Ɗan Wasan Arsenal Nwaneri Ya Wakilci Ƙasar
Published: 5th, April 2025 GMT
Babban kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya amince cewa zai yi wuya a shawo kan matashin dan wasan gaban Arsenal Ethan Nwaneri ya buga wa Nijeriya wasa, an haifi Nwaneri a Kasar Ingila amma kuma mahaifinshi dan Nijeriya ne yayin da mahaifiyarsa ta ke ‘yar Ingila.
Dan wasan mai shekaru 18 ya riga ya bugawa Ingila wasa amma har yanzu yana iya sauya sheka zuwa Nijeriya, Chelle ya yi ikirarin cewa kocin tawagar Ingila da ake wa lakabi da Three Lions, Thomas Tuchel, shi ma ya na sha’awar ya yi amfani da dan wasan mai buga gaba a matakin kasa.
Chelle ya shaida wa SCORENigeria cewa “A lokacin tafiyata zuwa Ingila (don ganawa da taurarin Nijeriya irin su Aled Iwobi da Wilfred Ndidi), na ce zan so Nwaneri ya buga wa Nijeriya wasa.”
“Saboda haka ina fatan hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFF) za ta yi magana da shi, sannan ni ma zan yi magana da shi, domin shawo kansa zai yi wahala saboda Ingila ma za ta so ta mayar da shi cikakken dan wasanta dake buga wasannin kasa da kasa, amma na yi imanin zan iya gamsar da shi saboda zan yi magana da shi game da yanayin wasan da kuma abin da ya dace bayan NFF ta tuntuve shi”.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.
Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a ChinaUwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.
Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.
Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.