Mai bai wa jagoran juyin musulunci na Iran shawara Dr. Ali Larijani ya ce, idan har Amurka da Isra’ila su ka fake da batun shirin makamashin Nukiliyar Iran na zaman lafiya, su ka kawo mata hari, to ya zama wajibi a gare ta ta kera makaman Nukiliya.

Dr. Ali Larijani wanda tashar talabijin din Iran ta yi jira da shi a jiya Litinin da dare, ya bayyana cewa; manyan kasashen duniya suna son yin alaka kai tsare da Iran cikin ‘yanci, sai dai suna da fuskantar matsin lamba daga Amurka.

Tsohon shugaban Majalisar shawarar musulunci ta Iran ya kuma kara da cewa; Idan har Amruka da HKI su ka kawo wa Iran hari, to, za ta dau hanyar kera makaman Nukiliya, kuma su kansu al’ummar kasa abinda za su so ganin ya faru kenan.

Dr. Ali Larijani wanda memba ne a cikin majalisar fayyace maslahar tsaron musulunci, ya kara da cewa; Yaki da Iran ba abu ne mai sauki ba, yana da tattare da hatsarin da zai koma kan mahara.

Larijani ya kuma ce; Fatawar Jagora ita ce, ta haramta mallakar makamin Nukiliya,amma idan Amurka ta yi kuskure, to matsin lambar mutane zai sa Iran ta kama hanyar kera makaman Nukiliya.

Har ila yau, Larijani ya ce; Fasahar Nukiliya da Iran take da ita, an tsara ta akan cewa, ko da an kawo wa Iran din hare-hare, to za ta ci gaba da aiki ba tare da tsaiko ba. Kum su kansu masu hankali daga cikin makiya sun san cewa idan su ka kawo wa Iran farmaki, to kuwa za ta daura damarar kera makaman Nukiliya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kera makaman Nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi kakkausar suka ga sabbin takunkuman da Amurka ta kakabawa kasarta

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i, ya yi kakkausar suka kan matakin da Amurka ta dauka na kakabawa wasu gungun mutane, hukumomin shari’a da jiragen ruwa masu alaka da makamashi da man fetur na Iran sabbin takunkumi.

Baqa’i ya gwada rashin amincewar Iran da bakar siyasar Amurka da na ‘yan sahayoniyya musamman farmakin da Amurka da gwamnatin sahayoniyya suka kaddamar na baya-bayan nan kan kasar Iran, yana mai bayyana kakaba takunkumin a matsayin baya da wani harumi na doka kawai matakin zalunci ne kan Iran lamarin da ke fayyace kiyayyar Amurka karara kan Iran.

Baqa’i ya kara da cewa: Al’ummar Iran suna sane da mummunar manufar wadannan tsauraran takunkumin da suke da nufin raunana Iran da neman take mata kowane irin hakki, za su tsaya da dukkan karfinsu wajen kalubalantarsu domin kare mutunci da muradunsu.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada cewa: Dabi’ar da Amurka take gudanarwa na nuna son kai da kuma bin hanyar da ba ta dace ba da tilastawa wajen cimma haramtattun manufofinta a matakin kasa da kasa, da kuma rashin mutunta tsarin doka da ‘yancin bil Adama, sun yi hannun riga da tushen dokokin kasa da kasa, gami da ka’idar mutunta ‘yancin kasashe da ‘yancin cinikayya tsakanin kasashe, da kuma daukan matakan nuna barazana ga duniya da ba a taba gani ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza