Arakci: Abokan Gaba Za Su Yi Nadamar Yi Wa Iran Barazana
Published: 1st, April 2025 GMT
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Arakci ya bayyana cewa, duk wata barazana da za a yi wa Iran za ta sa makiya su yi babbar nadama.
A wata hira a tashar talabijin din almasirah ta kasar Yemen ta yi da shi, ministan harkokin wajen na Iran ya ce, farfagandar da ake yi ta cewa, kai wa kasar Yemen hari share fage ne na yaki da Iran ba sabon abu ba ne, an sha yin irin wannan barazanar a baya.
Abbas Arakci ya kara da cewa; Iran ba za ta taba kyale duk wani mahaluki da zai rika yin Magana da ita da harshe na barazana ba, sannan ya kara da cewa makiya za su yi nadamar wannan barazanar.
Da yake Magana akan cigaba da kai wa Yemen hare-hare da Amurkan take yi, ministan harkokin wajen na Iran ya ce, nasarar da Yemen din take samu ne ya sa hakan take faruwa,kuma a cikin shekaru 10 na hare-haren da ake kai wa Yemen har yanzu an kasa yin galaba akan ta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
Wani babban jami’in sojan Iran ya ce an kai hare-hare a kalla wurare 150 a farmakin ramuwar gayya kan gwamnatin Isra’ila, ciki har da wasu sansanonin soji masu matukar muhimmanci.
Da yake zantawa da gidan talabijin na kasar da sanyin safiyar Asabar, Birgediya Janar Ahmad Vahidi, babban mai ba da shawara ga babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya ce, rundunar ta IRGC ta yi nasarar aiwatar da shirinta na Operation True Promise III.
A cewar kwamandan na IRGC, an kuma kai hari kan ma’aikatar harkokin soji da cibiyoyin soji da masana’antu a lokacin da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke daukar fansa.
Daga cikin wadanda harin ya rutsa da su sun hada da Manjo Janar Mohammad Bagheri, babban hafsan hafsoshin sojojin Iran, Birgediya Janar Amir Ali Hajizadeh, shugaban sashin kula da sararin samaniyar IRGC, da Manjo Janar Gholam-Ali Rashid, kwamandan babban shalkwatar Khatam al-Anbiya ta kasar.
Har ila yau, hare-haren sun yi sanadin mutuwar tsoffin masana kimiyyar nukiliya Mohammad-Mehdi Tehranchi, Fereydoun Abbasi, da Dr. Abdol-Hamid Minoucher, tare da fararen hula fiye da 70 da suka hada da yara da mata.
Duk da haka, ya sake nanata cewa wannan babban “kuskure” ne daga bangaren Isra’ila, yana mai gargadin cewa, “Dole ne su jira sakamakon.