Aminiya:
2025-11-02@17:11:28 GMT

Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta

Published: 30th, March 2025 GMT

Ƙungiyar Hamas ta ce tana goyon bayan komawa yarjejeniyar tsagaita wuta a Zirin Gaza, tana mai cewa za ta yi amfani da shawarar da masu shiga tsakanin suka bayar wadda za ta kai ga sakin ƙarin fursunonin Isra’ila biyar da kuma tsagaita wuta a Gaza tsawon kwana 50.

Babban jami’in Hamas da baya zaune a Gaza, Khalil al-Hayyam, ya ce ƙungiyar ta amince da ƙudirin da masu shiga tsakani daga Masar da kuma Qatar suka gabatar.

Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone Ladubban Ranar Idin Karamar Sallah

Ofishin firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ma ya ce ya karɓi tayin, amma ya gabatar da nasa tayin ”wanda ya ci karo da wanda masu shiga tsakanin suka gabatar masa, a ƙarƙashin jagorancin Amurka.”

BBC ya ruwaito cewa idan har ya tabbata, sabon shirin tsagaita wutar ya zo daidai da bakin ƙaramar Sallah da musulmai suka fara a ranar Lahadi.

A ranar Asabar, ofishin Nethanyahu ya ce ya yi zaman tuntuɓa game da sabon tayin da masu shiga tsakani suka gabatar masa.

Ya kuma ce ya gabatar da nasa sharaɗin, wanda Amurka ta yi amanna da shi, duk da cewa ofishin bai yi ƙarin bayani a kai ba. Itama Amurka ba ta kai ga cewa komai ba a kai kawo yanzu.

Wannan na zuwa ne yayin da dakarun Isra’ila suka ƙaddamar da sabbin hare-hare a Rafah da sassan Gaza bayan ƙarewar wa’adin tsagaita wutar da aka ƙulla a ranar 19 ga watan Janairu tsakanin ɓangarorin.

Tun bayan ƙarewar wa’adin har yanzu ɓangarorin sun gaza amincewa da fara aiwatar da zango na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar.

A zangon farko na yarjejeniyar tsagaita wutar dai Hamas ta saki ƴan Isra’ila 33, kuma har yanzu tana ci gaba da riƙon wasu 59, duk da dai ana zaton wasu daga cikin su sun mutu.

A baya dai Hamas ta haƙiƙance kan aiwatar da yarjejeniyar a yadda take tun farko, da kuma tattauna zango na biyu wanda zai kai ta ga sakin sauran mutanen da ta yi garkuwa da su, da kuma kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya ta hanyar janyewar dakarun Isra’ila daga Gaza.

Sai dai Isra’ila da Amurka sun nemi a tsawaita wa’adin zangon farko na yarjejeniyar wanda ya ƙare a watan da ya gabata, ba tare da fayyace yadda za a kawo ƙarshen yaƙin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila tsagaita wutar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Shugaba Bola Tinubu ya yi wa sabbin Shugabannin Sojoji ado da karin girma domin su dace da sabbin muƙamansu. Sabbin shugabannin rundunar sojin kasar da aka yi wa ado sun hada da Laftanar Janar, wanda yanzu ya zama Janar Olufemi Olatubosun Oluyede, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS); da kuma Manjo Janar yanzu ya koma Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye Undiendeye a matsayin Babban Hafsan Tsaro na farin kaya (CDI). Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  Sauran su ne Manjo Janar, wanda yanzu ya zama Laftanar Janar Waidi Shaibu a matsayin Babban Hafsan Soja (COAS); Air Vice Marshal, wanda yanzu ya zama Air Marshal Kevin Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama; da kuma Rear Admiral, wanda yanzu ya zama Vice Admiral Idi Abbas a matsayin Babban Hafsan Sojan Ruwa. Shugaba Tinubu ya sanar da maye gurbin Shugabannin Rundunar tsaron ne a ranar Juma’ar da ta gabata, wani mataki da aka danganta da bukatar sake mai da hankali da kuma karfafa tsaron kasa. Bayan haka, Shugaba Tinubu ya bukaci sabbin Shugabannin Rundunar tsaron da su dauki mataki mai tsauri kan barazanar tsaro da ke tasowa a fadin kasar, yana mai gargadin cewa ‘yan Nijeriya na tsammanin ganin sakamako, ba uzuri ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai