Aminiya:
2025-05-01@04:22:14 GMT

Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta

Published: 30th, March 2025 GMT

Ƙungiyar Hamas ta ce tana goyon bayan komawa yarjejeniyar tsagaita wuta a Zirin Gaza, tana mai cewa za ta yi amfani da shawarar da masu shiga tsakanin suka bayar wadda za ta kai ga sakin ƙarin fursunonin Isra’ila biyar da kuma tsagaita wuta a Gaza tsawon kwana 50.

Babban jami’in Hamas da baya zaune a Gaza, Khalil al-Hayyam, ya ce ƙungiyar ta amince da ƙudirin da masu shiga tsakani daga Masar da kuma Qatar suka gabatar.

Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone Ladubban Ranar Idin Karamar Sallah

Ofishin firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ma ya ce ya karɓi tayin, amma ya gabatar da nasa tayin ”wanda ya ci karo da wanda masu shiga tsakanin suka gabatar masa, a ƙarƙashin jagorancin Amurka.”

BBC ya ruwaito cewa idan har ya tabbata, sabon shirin tsagaita wutar ya zo daidai da bakin ƙaramar Sallah da musulmai suka fara a ranar Lahadi.

A ranar Asabar, ofishin Nethanyahu ya ce ya yi zaman tuntuɓa game da sabon tayin da masu shiga tsakani suka gabatar masa.

Ya kuma ce ya gabatar da nasa sharaɗin, wanda Amurka ta yi amanna da shi, duk da cewa ofishin bai yi ƙarin bayani a kai ba. Itama Amurka ba ta kai ga cewa komai ba a kai kawo yanzu.

Wannan na zuwa ne yayin da dakarun Isra’ila suka ƙaddamar da sabbin hare-hare a Rafah da sassan Gaza bayan ƙarewar wa’adin tsagaita wutar da aka ƙulla a ranar 19 ga watan Janairu tsakanin ɓangarorin.

Tun bayan ƙarewar wa’adin har yanzu ɓangarorin sun gaza amincewa da fara aiwatar da zango na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar.

A zangon farko na yarjejeniyar tsagaita wutar dai Hamas ta saki ƴan Isra’ila 33, kuma har yanzu tana ci gaba da riƙon wasu 59, duk da dai ana zaton wasu daga cikin su sun mutu.

A baya dai Hamas ta haƙiƙance kan aiwatar da yarjejeniyar a yadda take tun farko, da kuma tattauna zango na biyu wanda zai kai ta ga sakin sauran mutanen da ta yi garkuwa da su, da kuma kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya ta hanyar janyewar dakarun Isra’ila daga Gaza.

Sai dai Isra’ila da Amurka sun nemi a tsawaita wa’adin zangon farko na yarjejeniyar wanda ya ƙare a watan da ya gabata, ba tare da fayyace yadda za a kawo ƙarshen yaƙin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila tsagaita wutar

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta gano ma’aikatanta 240 da ke ƙarɓar albashi sau biyu a duk wata, da wasu 217 da ke amfani da lambar tantance asusun banki (BVN) guda ɗaya.

Wani mai magana da yawun gwamnati, Dakta Sulaiman Wali Sani, ya gaya wa manema labarai a ranar Lahadi cewa an gano wannan badaƙalar ce a yayin da ake tantance tsarin biyan albashin gwamnati.

Dr. Sani ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin biyan ma’aikata daidai kuma akan lokaci, kuma gano waɗannan matsalolin wani ɓangare ne na gyara al’amura.

Ya ce sun duba bayanan ma’aikata ta hanyar amfani da hotunan yatsa a matakin jiha da ƙananan hukumomi.

“Tsohuwar hanyar biyan mutane tana da matsaloli. Mun gano ma’aikata 240 suna karɓar albashi sau biyu kuma mutane 217 suna amfani da BVN ɗaya, wanda zai iya nufin akwai ma’aikatan bogi ko kuma mutane suna amfani da BVN na wani,” in ji Dakta Sani.

Ya kuma ce ma’aikata 1,335 ba su zo don a tantance su ba a tsawon fiye da watanni shida, wanda ya sa suke tunanin ko waɗannan mutanen da gaske suna aiki da gwamnati.

Alhaji Umar Idi, wanda ya duba biyan kuɗin ƙananan hukumomi, ya ce sun gano sunaye 247 da babu tabbaci a kansu. Waɗannan sun haɗa da mutanen da suka yi ritaya, waɗanda suka mutu, ko kuma waɗanda aka ci gaba da biyan su ba tare da izini ba bayan lokacin barinsu aiki.

“Daga cikin waɗannan ma’aikata 247, takwas ne kawai suka zo don tabbatar da cewa har yanzu suna aiki. Za a goge sauran sunaye 239, wanda zai rage wa gwamnati asarar naira miliyan 27 a duk wata,” in ji shi, yana mai cewa za a mayar da kuɗaɗen da aka samu ga asusun gwamnati.

Dakta Sani ya ce gwamnati ba ta ƙoƙarin hukunta kowa ba, kawai dai tana gyara tsarin ne don ma’aikata na gaske da ’yan fansho su ci gaba da karɓar haƙƙoƙinsu ba tare da wata matsala ko yanka ba bisa ƙa’ida ba.

“Tun lokacin da Gwamna Abba ya fara aiki, ya tabbatar da cewa ana biyan ma’aikatan gwamnati da ’yan fansho a kan lokaci, ba tare da ɓoyayyun cire-cire da aka riƙa yi a baya ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa yanzu da suke tsaftace tsarin biyan kuɗi, ma’aikata su yi tsammanin samun biyan kuɗi mafi inganci a gaba.

Gwamnati ta ce za ta ci gaba da magana da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa an magance duk matsalolin kuma jama’a sun sake amincewa da ayyukan gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut