HausaTv:
2025-06-15@19:30:09 GMT

Miliyoyin mutane sun gudanar da jerin gwanon ranar Qudus

Published: 28th, March 2025 GMT

Miliyoyin al’umma daga sassa daban daban na duniya sun gudanar da jerin gwanon zagayowar ranar Kuds ta duniya wacce ta gudana yau.

An dai kebance ranar ce domin nuna goyan baya ga al’ummar falasdinu, kuma ana gudanar da ita ne a ko wacce Juma’ar karshe ta watan ramadana bisa fatawar jagoran juyin juya halin musulinci na Iran Ayatollah Khumeiny.

A Iran ma kamar sauren sassan duniya jama’a sun fito kan tituna domin gudanar da bukukuwan ranar Qudus ta duniya, inda suke bayyana goyon bayansu ga Falasdinawa tare da yin tir da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a zirin Gaza.

An kuma yi irin wannan gangamin a kasashe da dama na yankin yammacin Asiya da suka hada da Iraki da Yemen da Lebanon da kuma wasu da dama a fadin duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Hukumar Kula da Yanayi (NiMet), ta sake fitar da gargaɗi game da yiwuwar ambaliyar ruwa a wasu jihohin a daminar bana.

A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, hukumar ta bayyana cewa Jihar Akwa Ibom ce ke fuskantar barazana mafi tsanani a halin yanzu.

Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran

Sauran jihohin da abin ka iya shafa sun haɗa da Sakkwato, Zamfara, Filato, Yobe, Bauchi, Bayelsa, Nasarawa, Binuwai, Ogun, Ekiti, Delta da kuma Ribas.

NiMet ta shawarci al’umma, musamman waɗanda ke zaune a cikin waɗannan jihohin, da su tabbatar sun yashe magudanan ruwa domin bai wa ruwa hanyar wucewa.

Haka kuma ta buƙaci mutane da su nisanci wuraren da ke da hatsarin ambaliya, kuma idan ruwa ya fara ƙarfi, su bar irin waɗannan wuraren domin kare lafiyarsu.

Ambaliya dai na daga cikin manyan matsalolin da ke janyo asarar rayuka da dukiyoyi a Najeriya a duk shekara.

A makonnin baya, garin Mokwa da ke Jihar Neja ya fuskanci ambaliya wadda ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 230.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025