Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
Published: 27th, March 2025 GMT
A Jamhuriyar Nijar, an daga martabar Abdourahmane Tiani madugun juyin mulkin sojin kasar daga mukamin Birgediya Janar zuwa Janar, mukamin soji mafi girma a kasar.
An ba Abdourahmane Tiani wannan mukamin ne bayan tabbatar masa da mukamin shugaban rikon kwarya na kasar a bikin da aka gudanar a jiya Laraba a Yamai babban birrin kasar.
Kafin hakan kuma Janar Abdourahamane Tiani, ya sa hannu kan dokar tsarin mulki na wucin gadi, mai taken “Tsarin farfado da Nijar”.
Bisa wannan doka, Tiani zai jagoranci kasar tsawon shekaru 5 tun daga ranar kaddamar da dokar, yayin da ainihin wa’adinta zai danganta da halin tsaro, da bukatun farfadowar kasar, da kuma ajandar kawancen kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso.
Hukumomin wucin gadin sun kunshi shugaban jamhuriyar Nijar, da kwamiti mai kula da harkokin tsaron kasar, da gwamnati da kwamitin sulhu, da hukumar sa ido kan harkar jin kai da sauransu.
Wata dokar kuma da shugaban rikon kwaryar ya sanya wa hannu a jiya ita ce ta rusa dukkanin jam’iyyun siyasa a duk fadin kasar.
An amince da wannan sabon tsarin mulki ne bisa kudurorin da aka tattara, a yayin taron farfado da kasa da aka gudanar a tsakanin ranakun 15 zuwa 19 ga watan da ya gabata a birnin Yamai, fadar mulkin kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A GhanaSai dai, abin dubi a nan shi ne, yadda kusan yanzu a kasar, tabbatar da doka da oda, a cikin kasar, ya koma kachokam, a huunun sojin.
ɗuba da sashe na 217 na kudin tsarin mulikin Nijeriya na 1999 da aka sabunta, wannan sashen, ayyukan soji tun daga na matakin rundunar sojin kasa da ta ruwa da kuma ta sama shi ne tabbatar da bai wa Nijeriya kariya, daga duk wani nau’in hare-haren, da ka iya zuwa, daga ketare, musamman ta hanyar, bai wa iyakokin kasar kariya, musamman bayan shugban kasa, ya bayar da umarnin yin hakan, tare da yarjewar, gammaiyyar Majalisun kasar.
Amma a nan, kamar yadda kudin tsarin mulkin kasa ya fayyace, sojin ba su da wani hurumin, maido da doka da oda, a cikin kwayar kasar.
Sai dai, shugaban kasa na da ikon umartar shigo da soji kan batun dawo da doka oda, domin su taimaka wa ƴansanda.
Wannan kiran na a yiwa tsarin ɗaukar kuratan ƴansandan, za a iya cewa, tsohon batu ne, kusan tun a Jamhuriyya ta hudu ta kasar nan.
Ko da yake dai, wasu gwamnatocin baya, sun yi yunkurin yiwa tsarin garanbawul, sai dai, ba a yi, wani abin azo a gani, kan batun ba.
Misali, tsohowar gwamnatin tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo a 2006, ta kafa wani kwamati na Fadar shugaban kasa, da ɗan Mandami ya jagoranta, domin a samar da sauye-sauye, a aikin ƴansanda.
Bugu da kari, a lokacin mulkin marigayi tsohon shugaban kasa Umaru Yar’Adua a 2008, ya kafa kwamtin Fadar shugaban kasa, karkashin shugabancin Muhammadu ɗikko Yusuf.
Kazalika, a 2012 tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kafa kwamtin Fadar shugaban kasa, a karkashin shugabanci Parry Osayande.
A 2018 an kafa kwamitin Fadar shugaban kasa na samar da sauyi kan batun dakarun ƴansanda da ke yakar masu yin fashi da makami wato SARS.
Sai dai, duk irin wannan kokarin da aka yi a baya, matsalar ba sake Zane ba
A nan muna nuna damuwarmu, kan rashin samar da tsarin da ya dace, na yin sauye-sauye a aikin na ƴasanda.
Ra’ayin wannan Jaridar, ya zo daidai da cewa, batu daya da ke kawo cikas kan samar da ingantaccen tsari a aikin na ƴansanda shi ne, na rashin kyakyawan ɗaukar jami’an aikin.
ɗukkan irin sauye-sauyen da za a samar na ɗaukar kuratan, zai yi wuya a cimma wata nasarar kirki, matukar tsarin na ɗaukar kuratan, ya ci gaba da zama, ana yinsa, ba bisa ka’ida ba.
Batun ɗaukar kuratan ba abu ne na was aba, dole ne rinka ɗaukar kuratan, masu halayya ta gari ba masu kashi a gindi ba.
Idan za a iya tunawa, a 2024, an tayar da Jijiyar Wuya a tsakanin rundunar ƴansanda ta kasa da Hukumar kula da aikin ƴan sanda na kasa, kan batun ɗaukar kurata sama oɓer 10,000 da kuma ɗaukar, kurata na musamman.
An ruwaito Kakakin runudanar ƴansanda na kasa ACP Olumuyiwa Adejobi, ya shelanta cewa, ɗaukar wadanan kuratan na cike da kura-kurai da dama da aka tabka, ciki har da na zargin cin hanci, har da kuma sanya sunayen wasu, da ma ba su nemi shiga aikin ba, wasun kuma, ba su iya tsallake gwaje-gwajen da aka yi masu na kiwon lafiyarsu ba.
Hakazalika, a 2022 a lokacin mulkin toshon shugaban kasa marigayi Muhammadu Buhari, gwamnatinsa ta kirkiro da sabon tsari ga aikin, musamman domin a tabbatar da an inganta aiki yadda zai iya yakar duk wani nau’I, na aikata manyan laifuka da kare rayukan yan Nijeriya da kuma dukiyoyinsu a karkashin doka ta 2020.
Sai dai, duk da hakan, wannan manufar, hakar bata cimma ruwa ba, musamman kan batun ɗaukar ingantattun kuratan.
Kazalika, a kwanan baya, Ma’aikatar Kula da Jindadi da Walwalar ƴansanda tare da hadaka da rundunar ƴansanda ta kasa, ta kaddamar da kudurin farfado da aikin ƴansanda.
Sai dai, Ma’aikatar a cikin wannan kudirin, ba ta tabo batun tsarin yin garanbawul kan ɗaukar kuratan ba.
Ko da yake dai, wannan Jaridar ta jinjinawa wannan kokarin na mahukuntan ƴansandan da suka yi a baya, amma Jaridar, na da ra;ayin cewa, dole ne a samar da kyakyawan tsari na ɗaukar kuratan ƴansandan, musamman a tabbatar da ba dauki wadanda ke wani guntun kashi, na aikata laifi ba. Yin hakan shi ne, babban ginshiki kuma madogararmu, a nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp