Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
Published: 25th, March 2025 GMT
Yansanda a kasar Turkiyya suna ci gaba da fafatawa day an adawa masu goyon bayan magajin garin birnin Istambul Ekram Imam oglu.
Tashar talabijin ta Al-mayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa magajin garin na birnin Istambul yana daga cikin fitattun masu adawa da gwamnatin Urdugan, sannan a halin yanzu jami’an sharia a kasar sun bada sanarwan cewa sun kammala bincike a kansa, kuma nan ba da dadewa ba zasu gurfanar da shi a gaban kotu don fuskantar shari’a.
A ranar laraban da ta gabat ce gwamnatin kasar Turkiya ta bada umurnin kama Ekram Imam oglu magajin garin birnin Istambul tare da zarginsa da cin hanci da rashawa da kuma ayyukan ta’addanci. Wanda ya musanta hakan a yanke.
Har’ila yau masu gabatar da shari’a a kasar sun bukaci a ci gaba da tsare magajin garin har zuwa lokacinda za’a fara shari’arsa a cikin yan kwanaki masu zuwa. Tun ranar laraban da ta gabace yan sanda a birnin istambul da kuma wasu birane a kasar suke fafatawa da dubban daruruwan magoya bayan Imam oglu wadanda suke bukatar a sake shi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: magajin garin
এছাড়াও পড়ুন:
‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
Jami’an diflomasiyya a Tanzania sun ce akwai kwararan hujjoji da ke tabbatar da an kashe akalla mutum 500 a cikin kwana biyu da barkewar zanga-zangar kin amincewa da sakamakon zaben da aka gudanar a ranar Laraba.
Sai dai a wani bangaren kuma, alkalumman Yan’adawa sun zarta haka.
Wakiliyar BBC ta ce ministan harakokin wajen Tanzania Mahmoud Kombo Thabit ya musanta rahotannin, amma wani jagoran adawa John Kitoka ya ce ‘yansanda da wasu sojojin haya na kasashen waje ne suka aiwatar da kisan mutane cikin dare.
Majalisar Dinkin Dauniya ta yi kiran gudanar da bincike kan zargin amfani da karfin da ya wuce kima a kan masu zanga-zangar.
BBC