Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
Published: 25th, March 2025 GMT
Yansanda a kasar Turkiyya suna ci gaba da fafatawa day an adawa masu goyon bayan magajin garin birnin Istambul Ekram Imam oglu.
Tashar talabijin ta Al-mayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa magajin garin na birnin Istambul yana daga cikin fitattun masu adawa da gwamnatin Urdugan, sannan a halin yanzu jami’an sharia a kasar sun bada sanarwan cewa sun kammala bincike a kansa, kuma nan ba da dadewa ba zasu gurfanar da shi a gaban kotu don fuskantar shari’a.
A ranar laraban da ta gabat ce gwamnatin kasar Turkiya ta bada umurnin kama Ekram Imam oglu magajin garin birnin Istambul tare da zarginsa da cin hanci da rashawa da kuma ayyukan ta’addanci. Wanda ya musanta hakan a yanke.
Har’ila yau masu gabatar da shari’a a kasar sun bukaci a ci gaba da tsare magajin garin har zuwa lokacinda za’a fara shari’arsa a cikin yan kwanaki masu zuwa. Tun ranar laraban da ta gabace yan sanda a birnin istambul da kuma wasu birane a kasar suke fafatawa da dubban daruruwan magoya bayan Imam oglu wadanda suke bukatar a sake shi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: magajin garin
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
A jiya Litinin ne dai gwamnatin kasar Holland ta sanar da hana wa minstocin tsaron kasa Itmir Bin Gafir, da na kudi, Bitsirael Smotrich shiga cikinta.
Kasar ta Holland ta zargi wadannan mutanen biyu da cewa suna ingiza sojojin HKI da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi da kuma fadada yawan matsugunan ‘yan sahayoniya a yankunan da aka ce nan ne za a kafa Daular Falasdinawa.
Haka nan kuma gwamnatin kasar ta Holland ta kira yi jakadan HKI a birnin Hauge domin gargadinsa akan yanayin da ake ciki a Gaza, da cewa babu yadda za a iya ci gaba da jurewa akansa, ko kare dalilin jefa yankin cikin wannan halin.”
Wannan matakin na kasar Holland ya zo ne gabanin wani taro da tarayyar turai za ta yi a yau Talata domin jingine aikin tare da HKI a fagen nazari da bincike na ilimi, saboda ta ki tsagaita wutar yaki a Gaza.
Tun da fari, Fira ministan kasar Holland Dick Schoof ya wallafa a sharin X cewa; A yayin taron da kasashen turai za su yi, Kasarsa za ta yi matsin lamba akan ganin an dakatar da yarjejeniyar kasuwanci da HKI, haka nan kuma kakaba takunkumai akan shigar da kayanta na kasuwanci zuwa kasuwannin turai.
Fira ministan na kasar Holland ya ce, ya fada wa shugaban HKI Ishaq Herzog wannan matakin da suke son dauka ta hanyar tarayya turai.