HausaTv:
2025-05-01@04:47:31 GMT

UNRWA : hana shigar da kayan agaji Gaza, ya jefa yankin cikin matsanancin hali

Published: 25th, March 2025 GMT

Shugaban hukumar kula da ‘yan gudun hijira falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya (UNRWA) ya yi gargadin cewa hana shigar da kayayyakin jin kai da Isra’ila ta yi a zirin Gaza ya jefa yankin cikin mawuyacin hali na rashin abinci.

“Makonni uku kenan da hukumomin Isra’ila suka hana shigar da kayayyaki cikin Gaza.

“Ba abinci, ba magani, ba ruwa, babu man fetur,” inji Philippe Lazzarini a cikin wani sako a shafukan sada zumunta.

Tun a ranar 4 ga watan Maris ne Isra’ila ta hana shigar da kayan agaji zuwa Gaza, bayan karewar kashi na farko na tsagaita bude wuta a yarjejeniyar da ta cimma da kungiyar gwagwarmayar falasdianwa ta Hamas data kunshi musayar fursunoni tsakanin bangarorin.

Lazzarini ya jaddada cewa al’ummar Gaza sun dogara ne kan shigo da kayayyaki daga yankunan da aka mamaye.

“Duk ranar da ta wuce ba tare da agajin jin kai ba, hakan na nufin yara da yawa suna kwana da yunwa, cututtuka na yaduwa,” in ji babban jami’in UNRWA.

Lazzarini ya bayyana haramcin taimakon a matsayin wani hukuncin bai daya ga al’ummar Gaza, wadanda akasarinsu kananan yara ne da mata.

Ya yi kira da a dage wannan kawanya da kuma kai agajin jin kai da kayayyakin kasuwanci zuwa Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hana shigar da

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut

Jiragen yakin HKI sun kai hari a yankin Hangara dake unguwar “Dhahiya” a cikin birnin Beirut. Yankin da jiragen yakin na ‘yan sahayoniya su ka kai wa harin, yana cike da mutane da kuma makarantu biyu.

Jiragen yakin na HKI sun harba makamai masu linzami 3, da hakan ya haddasa tashin gobara.

A sanadiyyar wannan harin, an sami shahidi daya,yayin da wasu da dama su ka jikkata.

A ranar 1 ga watan Aprilu ma dai sojojin HKI sun kai wani harin a unguwar Dhahiya wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane 4 da kuma jikkata wasu da dama.

Tun bayan tsagaita wutar yaki a ranar 27 ga watan Aprilu 2025, HKI ta keta wutar yakin fiye da 2000.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut