HausaTv:
2025-11-03@04:58:40 GMT

Senegal ta yi Allah-wadai da tsare ‘yan kasarta a Mauritania

Published: 14th, March 2025 GMT

Ministar Harkokin Wajen Senegal, Yacine Fall, ta ce hukumomin kasarta sun bayyana rashin jin dadi game da tsare ‘yan Senegal da kuma tilasta musu barin kasar bisa zarginsu da zama cikin Mauritania ba bisa ka’ida ba.

Hukumomin kasar Mauritaniya sun kaddamar da wani gangamin korar bakin haure daga kasashen Afirka daban-daban.

A wani jawabi da ta gabatar yayin taron amsa tambayoyi a majalisar dokokin kasar ta Senegal kamar yadda kamfanin dillancin labaran Faransa Fall ya ruwaito,  “kowace kasa tana da nata dokoki, amma rashin samun takardar zama ko takardar izinin aiki a cikin sa ba zai taba hujja ta cin zarafi ba.

Majalisar dokokin kasar Senegal ta yi kira ga gwamnatin da ta gaggauta daukar matakai don ganin an warware matsalar a’yan kasar da suke zaune a Mauritania,” tana mai bayyana abin da Mauritania ke yi a matsayin “cin zarafin bil’adama.”

A nata bangaren, ma’aikatar harkokin wajen kasar Mauritaniya a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce kasar ta tabbatar da bude kofa ga bakin haure tare da karfafa tare da yin komai a cikin  tsari, da kuma shiga kasar cikin kasar bisa sharudda da suke a a kan doka, tana mai cewa “Mauritaniya tana maraba da baki da ke zama a cikin kasarta bisa doka kuma cikin yanayi mai kyau, musamman wadanda suka fito daga kasashe makwabta.”

Ta kuma yi nuni da cewa, yin kaura ba bisa ka’ida ba a wasu lokuta ya kan zama barazana ga yanayin zaman lafiya da tsaron kasa, a kan haka ne take kokarin tantance yanayin baki mazauna kasar, amma hakan ba zai yi tasiri a kan alakar da ke tsakaninta dad a kasashen dab akin suka fito ba, kuma za a warware batun  ta hanyar fahimtar juna.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Mai shari’a Dahiru ya amince da buƙatar, ya kuma ɗage shari’ar zuwa ranar 12 ga watan Disamba, 2025, domin ci gaba da sauraron shari’ar.

Ƙuli-ƙuli dai nau’in abin ci ne mai taushi da ake yi da gyaɗa, ana soyawa har sai ya zama ƙura-ƙura ta yadda za a ci cikin nishaɗi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku