Masu Goyon Bayan Falasdinu Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Don Bukatar Sakin Mahmoud Khalil A Tsakiyar Birnin New York
Published: 13th, March 2025 GMT
Amurkawa masu goyon bayan Falasdinu sun gudanar da gangami a unguwar manhatan na birnin Nuyork don neman sakin Mahmoud Khalil daya daga cikin masu gwagwarmaya kan tafarkin samun yencin Falasdinawa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kama Mahmoud Khalila da kuma tsareshi ya ingiza matasa da dama a Amurka suka nuna goyon bayansu a gareshi, wasu kuma suka fito zanga-zangar neman a sake shi.
Mahmoud Khalil dai, ya kammala karatunsa ne a Jami’ar Colombia na birnin News na kasar Amurka. Sannan ya shahara da goyon baya ga al-ummar Falasdinu. Banda haka yana da ‘Green Card wanda ya bashi damar zama a kasar Amurka na dindin din. Amma a rahotannin da suke fitowa gwamnatin kasar tan son soke dakardun nasa don basu damar korarsa daga kasar Amurka.
Gwamnatin shugaba Trump ta yanke Dalar Amurka miliyon $400 kasan Jami’ar Colombia saboda tursasa mata ta yi fada da wadanda ya kira, masu nuna kin yahudawa
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Yayin da taro na biyu na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya ke kara matsowa, sakamakon kuri’un jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, sun nuna gamsuwa da hadin gwiwa bisa matsayin koli dake tsakanin Sin da kasashen nan biyar na yankin tsakiyar Asiya, a matsayin wata hadaka ta al’umma mai kyakkyawar makomar bil’Adama, wadda ke kara shigar da sabon kuzari, na daidaito cikin yanayin duniya dake kara shiga yanayin tangal-tangal.
Tun dai taro na farko na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya, hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen biyar ya shiga wani sabon zango na ci gaba. Har ma kuri’un na jin ra’ayin jama’a suka nuna yadda kaso 90.4 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu, ke ganin tsarin taron shugabannin Sin da kasashen na tsakiyar Asiya ya taka rawar gani a wannan fanni.
Kazalika, kaso 92 bisa dari na ganin ta hanyar mayar da kasashen tsakiyar Asiya daya daga muhimman jigon diflomasiyyar makwaftanta, Sin ta samar da wasu damammaki ga kasashen tsakiyar Asiya, na cimma burin sauye-sauye, da ci gaba da yin babban tasiri a shiyyarsu. Yayin da yanayin yankunan Turai da Asiya ke kara sauyawa cikin hanzari, kaso 88.1 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu na ganin gina al’ummun Sin da tsakiyar Asiya masu makomar bai daya, na da muhimmancin gaske wajen karfafa tsare-tsaren kasashen tsakiyar Asiya, na samar da ‘yanci da daidaiton shiyyarsu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp