HausaTv:
2025-03-16@01:11:58 GMT

DRC Ta Sa Kudi Dalar Amurka Miliyan 5 Akan Jagororin ‘Yan Tawayen M 23

Published: 9th, March 2025 GMT

Gwamnatin jamhuriyar demokradiyyar congo ta ware kudi da sun kai dalar Amurka miliyan 5 akan duk wanda ya kamo mata shugabannin  kungiyar ‘yan tawaye ta M 23 da su ka hada Corneelle Nangaa, Sultani Makenga da kuma Betrand Bisimwa.

Sai dai duk da kudade masu tsokar da DRC din ta sanya akan shugabannin kungiyar su uku, abin da kamar wuya,saboda ganin yadda wannan kungiyar take ci gaba da kutsawa cikin manyan birane tana shimfida ikonta a cikinsu.

A halin yanzu biranen Goma da Bukavu da suke a gabashin wannan kasa sun shiga karkashin ikon mayakan kungiyar ta M 23.

Dubban mutane ne dai su ka rasa rayukansu yayin da wasu dubun dubata kuma su ka bar gidajensu zuwa inda za su tsira da rayukansu.

Shugaban kasar ta DRC Felix Tashisekedi ya kira yi kungiyoyin kasa da kasa da su kakaba wa kasar Rwanda takunkumi saboda yadda take goyon baya da kuma taimaka wa kungiyar M23 da take ci gaba da rike da biranen Goma da Bukavu.Da akwai sojojin Rwanda 4,000 da suke taimakawa ‘yan tawayen na M 23.

Shugaban kasar ta DRC ya zargi Rwanda da wawason albarkatun karkashin kasar da ake kiyasin cewa sun kai na biliyoyin daloli.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas ta yi Allah wadai da haramcin da Amurka da EU suka yi wa gidan talabijin na Al-Aqsa

Kungiyar Hamas ta yi Allah-wadai da matakin hadin gwiwa da Amurka da Tarayyar Turai suka dauka na hana watsa tashar talabijin ta Al-Aqsa ta Larabci ta Falasdinu da ke da alaka da kungiyar gwagwarmayar.

Kungiyar ta bayyana hakan a matsayin wani yunkuri na toshe muryar Falasdinawa.

Sanarwar da Hamas ta fitar ta kara da cewa, wannan shawarar toshe ‘yancin watsa labaru ne da kuma hakki na al’ummar Falasdinu na a ji muryarsu a duniya.”

Hamas ta yi kira ga cibiyoyin yada labarai na kasa da kasa da su yi Allah wadai da wannan shawarar, kuma kada su yi shiru dangane da cin zarafin da gwamnatin sahyoniya ta ke yi wa dokokin kasa da kasa da ka’idojin jin kai.

Bisa shawarar hadin gwiwa da Amurka da EU suka cimma, za a ci tarar duk wani sashe na tauraron dan adam da ke yada shirye shiryen tashar talabijin ta Al-Aqsa bisa zargin da ake mata na “yada ayyukan ta’addanci.”

Ita ma a nata bangaren, kungiyar Jihad Islami ta Falastinu ta yi tir da haramcin da aka yi wa tashar talabijin din ta Al-Aqsa, tana mai cewa wani hari ne da nufin murkushe muryar Falasdinu da kuma hana al’ummar kasar isar da sakonin ukubar da suke fuskanta ga duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Ba Jakadan Afirka ta Kudu Sa’o’i 72 Ya fice daga kasar
  • Hamas ta yi Allah wadai da haramcin da Amurka da EU suka yi wa gidan talabijin na Al-Aqsa
  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  •  Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  •  An Yi Gargadi Akan Rushewar Kungiyar  Agajin Falasdianwa Ta UNRWA
  • Taron Kasashen Iran, Rasha Da China A Birnin Beijing Ya Bukaci A Kawo Karshen Takunkumai Akan Tehran
  • Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500
  • Sojojin Iran Sun Ce A Shirye Suke Su Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana Ga Tsaron Kasar