HausaTv:
2025-11-14@10:29:14 GMT

DRC Ta Sa Kudi Dalar Amurka Miliyan 5 Akan Jagororin ‘Yan Tawayen M 23

Published: 9th, March 2025 GMT

Gwamnatin jamhuriyar demokradiyyar congo ta ware kudi da sun kai dalar Amurka miliyan 5 akan duk wanda ya kamo mata shugabannin  kungiyar ‘yan tawaye ta M 23 da su ka hada Corneelle Nangaa, Sultani Makenga da kuma Betrand Bisimwa.

Sai dai duk da kudade masu tsokar da DRC din ta sanya akan shugabannin kungiyar su uku, abin da kamar wuya,saboda ganin yadda wannan kungiyar take ci gaba da kutsawa cikin manyan birane tana shimfida ikonta a cikinsu.

A halin yanzu biranen Goma da Bukavu da suke a gabashin wannan kasa sun shiga karkashin ikon mayakan kungiyar ta M 23.

Dubban mutane ne dai su ka rasa rayukansu yayin da wasu dubun dubata kuma su ka bar gidajensu zuwa inda za su tsira da rayukansu.

Shugaban kasar ta DRC Felix Tashisekedi ya kira yi kungiyoyin kasa da kasa da su kakaba wa kasar Rwanda takunkumi saboda yadda take goyon baya da kuma taimaka wa kungiyar M23 da take ci gaba da rike da biranen Goma da Bukavu.Da akwai sojojin Rwanda 4,000 da suke taimakawa ‘yan tawayen na M 23.

Shugaban kasar ta DRC ya zargi Rwanda da wawason albarkatun karkashin kasar da ake kiyasin cewa sun kai na biliyoyin daloli.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi

Daga Bashir Meyere

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da bukatar Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, na neman rancen Naira Tiriliyan 1.15 domin cike gibin kasafin kudin shekarar 2025.

Amincewar ta biyo bayan gabatar da rahoton kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da lamuran bashi na cikin gida da na waje.

Yayin da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin, Sanata Aliyu Magatakarda Wamako, wanda mataimakinsa Sanata Haruna Manu ya wakilta, ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2025 na Naira tiriliyan 59.99 da Majalisar ta amince da shi, ya karu da Naira tiriliyan 5.25 idan aka kwatanta da Naira tiriliyan 54.74 da gwamnatin tarayya ta fara gabatarwa.

Ya ce an riga an amince da Naira tiriliyan 12.95 a cikin kasafin, wanda hakan ya bar gibin  Naira tiriliyan 1.147, abin da ya haifar da bukatar wannan shirin neman rance.

Kwamitin ya bai wa Majalisar shawarar  amincewa da rancen cikin gida na Naira tiriliyan 1.15 domin cike gibin da ya samo asali daga karin kudin kasafin.

Kwamitin ya kuma bukaci Ministar Kudi  da Ofishin Kula da Lamuran Bashi su tabbatar da cewa an aiwatar da rancen cikin tsari, tare da bin ka’idojin gaskiya,  da sharuɗɗan da suka dace.

Majalisar Dattawa ta kuma umurci kwamitinta mai kula da bashin cikin gida da na waje da ya rika sa ido kan yadda za a aiwatar da amfani da kudin da aka ciwo bashi.

Haka kuma, Ministar Kudi za ta rika mika rahoton kowane watanni uku kan halin da ake ciki, da amfani da kudaden, da yadda ake biyan basussuka, yayin da za a kai duk wani rahoton sabawa tsarin  ga Majalisar Dattawa domin daukar matakin doka da ya dace.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe
  • Faransa: An Fara Shari’ar Shugaban ‘Yan Tawayen DRC Bisa Laifuna Akan Bil’adama
  • MURIC ta buƙaci Tinubu ya sauke Amupitan daga shugabancin INEC
  • Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi
  • Tanzania: MDD Ta Yi Kira Da A Yi Bincike Akan Daruruwan Mutanen Da Aka Kashe Sanadiyyar Rikcin Zabe
  • Iran Ta Zama Memba A Kungiyar Tattara Bayanai Na  Ilimomi Da Kere-kere Ta Duniya ( ISKO)
  • Kungiyar Wamban Shinkafi Ta Amince Da Tinubu a 2027
  • Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam