Aminiya:
2025-05-02@05:01:28 GMT

Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadai

Published: 7th, March 2025 GMT

Ƙungiyar Shugabannin Kiristoci ta Kudancin Kaduna (SKCLA) ta yi tofin Allah tsine da kashe Rabaran Fada Sylɓester Okechukwu na Gundumar Katolika da ke Kafanchan, inda ta jingina haka ga taɓarɓarewar harkokin tsaro a yankin.

A cikin wata sanarwa da Shugaban SKCLA,  Dakta Emmanuel Nuhu Kure ya fitar a ranar Jumma’a ya miƙa ta’aziyyarsu ga Gundumar Katolika ta Kafanchan, tare da yin kira ga hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa a kan lamarin.

Fashewar tankar mai: Mutum 7 sun mutu, gonaki sun lalace a Neja An yi garkuwa da ɗan uwan ​​Bishop Kukah da wasu 6 a Kaduna

“Wannan mummunar aiki babbar asara ce ga Coci da matuƙar tayar da hankali da damuwa game da ci gaba da kai hare-hare ga shugabannin Kiristoci a Kudancin Kaduna,” in ji Kure.

 Inda ya koka da yawan kashe-kashen shugabannin addinin Kirista da suka yawaita, inda ya yi gargaɗin cewa ci gaba da kai wa malaman addini hari na iya ɗaukar wata ma’ana da ka iya rusa zaman lafiya a jihar. “Wataƙila ‘yan ta’adda masu aikata laifi ne ke aikata hakan, amma me ya sa ake kai wa ma’aikatan cocin hari su kaɗai?” inji shi.

SKCLA ta yi kira ga hukumomi da su tabbatar da anyi adalci ga malamin da aka kashe, tare da kiran mazauna yankin da su kasance masu sa ido game da abin da ya shafi tsaro sannan su riƙa sanar da hukumomi duk wani abu da ya bayyana musu.

Idan za a iya tunawa a ranar larabar da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga su kayi sace Faston Katolika mai suna Rabaran Fada Sylɓester Okechukwu a yankin Tachira da ke ƙaramar hukumar Ƙaura ta Jihar Kaduna inda suka kashe shi ba tare da buƙatar komai ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kaura

এছাড়াও পড়ুন:

 Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma

Manyan malaman addinin darikar Roman Katolika za su fara Shirin zabar shugaban darikar tasu a fadar Vatican

Adadin manyan malaman addinin masu mukamin “Cardinal” 130 ne za su taru a fadar Vatican, domin su zabi wanda zai maye gurbin Paparoma Farancis da ya rasu.

Sai dai masu kusancin da fadar ta Vatican suna bayyana cewa, da akwai batutuwa da dama da su ka raba kawunan manyan malaman addinin na Roman Katolika da  su ka batun auren jinsi, da rawar da mata za su taka a karkashin inuwar cocin.

Sai dai kuma wani mai sharhi akan abubuwan da su ka shafi cocin, Reese ya bayyana cewa, masu zaben za su mayar da hankali ne akan wanda zai kare ayyukan da mamacin Paparoma Francis ya bari.

Tare da cewa babu kafa ta yin yakin neman zabe a tsakanin masu mukamin na Cardinal, sai dai da akwai wasu siffofi da halaye da ake son gani da wadanda za su iya zama ‘yan takara.

Ana sanar da wanda ya zama sabon Paparoma ne ta hanyar samun kaso 2/3 na kuri’un da manyan masu zaben su ka kada.

A bisa ka’idar cocin, duk wanda aka yi wa wankan tsarki na  ” Baptisma”zai iya zama paparoma,amma  kuma tun daga 1378 ba a zabi wanda bai kai mukamin “Cardinal” ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa maso Gabas sun buƙaci a ɗauki mataki kan matsalolin yankin
  • Iran ta yi Allah-wadai da sabon takunkumin da Amurka ta lafta mata
  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana