Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadai
Published: 7th, March 2025 GMT
Ƙungiyar Shugabannin Kiristoci ta Kudancin Kaduna (SKCLA) ta yi tofin Allah tsine da kashe Rabaran Fada Sylɓester Okechukwu na Gundumar Katolika da ke Kafanchan, inda ta jingina haka ga taɓarɓarewar harkokin tsaro a yankin.
A cikin wata sanarwa da Shugaban SKCLA, Dakta Emmanuel Nuhu Kure ya fitar a ranar Jumma’a ya miƙa ta’aziyyarsu ga Gundumar Katolika ta Kafanchan, tare da yin kira ga hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa a kan lamarin.
“Wannan mummunar aiki babbar asara ce ga Coci da matuƙar tayar da hankali da damuwa game da ci gaba da kai hare-hare ga shugabannin Kiristoci a Kudancin Kaduna,” in ji Kure.
Inda ya koka da yawan kashe-kashen shugabannin addinin Kirista da suka yawaita, inda ya yi gargaɗin cewa ci gaba da kai wa malaman addini hari na iya ɗaukar wata ma’ana da ka iya rusa zaman lafiya a jihar. “Wataƙila ‘yan ta’adda masu aikata laifi ne ke aikata hakan, amma me ya sa ake kai wa ma’aikatan cocin hari su kaɗai?” inji shi.
SKCLA ta yi kira ga hukumomi da su tabbatar da anyi adalci ga malamin da aka kashe, tare da kiran mazauna yankin da su kasance masu sa ido game da abin da ya shafi tsaro sannan su riƙa sanar da hukumomi duk wani abu da ya bayyana musu.
Idan za a iya tunawa a ranar larabar da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga su kayi sace Faston Katolika mai suna Rabaran Fada Sylɓester Okechukwu a yankin Tachira da ke ƙaramar hukumar Ƙaura ta Jihar Kaduna inda suka kashe shi ba tare da buƙatar komai ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kaura
এছাড়াও পড়ুন:
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
Gwamna Inuwa ya kuma jaddada bukatar bin ka’idojin kariya a harkokin sufurin ruwa, inda ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomi, da shugabannin al’umma, da direbobin kwale-kwale da hukumomin da ke da ruwa da tsaki da sauran wadanda suka dace su kara kaimi wajen ganin ana kiyaye duk ka’idojin kariya don magance sake afkuwar ibtila’in a nan gaba.
Ya umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA) da Majalisar. Karamar Hukumar Nafada su bayar da duk wani tallafin da ya dace ga iyalan da abin ya shafa tare da hada hannu da hukumomin da abin ya shafa don inganta tsaro da wayar da kan al’ummomin da ke yankunan kogi.
Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’a yana mai cewa “A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga iyalan mamatan tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama ya gafarta musu kurakuransu, ya kuma saka musu da Aljannar Firdaus”.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA