An yi garkuwa da ɗan uwan Bishop Kukah da wasu 6 a Kaduna
Published: 7th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane sun yi garkuwa da mutane bakwai da suka haɗa da mata da ƙananan yara a ƙauyen Anchuna da ke masarautar Ikulu a ƙaramar hukumar Zangon Kataf a Jihar Kaduna.
An samu rahoton cewa harin wanda ya auku a daren ranar Larabar, ya jefa al’ummar yankin cikin firgici yayin da maharan suka mamaye ƙauyen da suke da yawa, inda suka yi ta harbe-harbe kafin daga bisani su tafi da su.
Wani mazaunin yankin mai suna Samuel Kukah, ɗan gidan fitaccen malamin kirista, Bishop Hassan Kukah, ya tabbatar wa wakilinmu faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa akwai ƙaninsa Ishaya Kukah na cikin waɗanda aka kama.
“Yayana Ishaya, shi kaɗai ne namiji a cikin waɗanda aka sace; sauran mata da yara ne, maharan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 11 na dare,” in ji shi.
Kukah ya ƙara da cewa har ya zuwa lokacin da yake zantawa da wakilinmu, babu wata tuntuɓa da masu garkuwar suka yi dangane da neman kuɗin fansa.
“Muna yi musu addu’ar Allah ya kare su yayin da muke jiran kowane kira,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ganin an dawo da waɗanda lamarin ya rutsa da su lafiya, yana mai jaddada cewa galibin waɗanda aka sace mutane ne masu rauni.
Da aka tuntuɓi jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya ce zai yi wa wakilinmu ƙarin bayani kan lamarin, amma har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ba.
Mazauna yankin na ci gaba da yin kira da a tsaurara matakan tsaro domin daƙile matsalar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
Iran ta kaddamar da wasu jerin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila a matsayin maida martani kan haren haren da Isra’ila ta kai wa kasar a cikin daren ranar Juma’a.
Bayanai sun ce hare-haren na Iran sun lalata gine-gine da dama da jikkata mutane yayin da wasu rahotannin ke cewa an samu hasarar rayuka na akalla mutum biyu.
A cewar rahotannin kafofin yada labaran Isra’ila daban-daban, makamai masu linzami na iran sun fada a yankunan Tel Aviv, Haifa, Beersheba da wasu wurare.
An bayar da rahoton barna mafi muni a birnin Tel Aviv, inda akalla makami mai linzami guda ya afkawa wani bene mai hawa 50, lamarin da ya janyo fashewar wani abu mai karfi wanda ya sa hayaki ya tashi a sararin samaniyar birnin.
A cewar darektan cibiyar nazarin dabarun da huldar kasa da kasa, Amir Al-Mousawi, daya daga cikin makami mai linzamin na Iran ya afkawa wata cibiyar binciken nukiliya da ke birnin Tel Aviv.
Wasu rahotanni sun ce an kuma yi nasarar kaiwa ma’aikatar harkokin sojan Isra’ila hari.
Gwamnatin kasar ta sanya takunkumi, inda ta umarci mazauna yankin da kada su buga hotuna ko bidiyo na wuraren da makami mai linzami na Iran ya kai hari, kamar yadda kafar yada labaran Isra’ila ta bayyana.
Birgediya Janar Ahmad Vahidi, da yake magana da gidan talabijin na iran, ya ce martanin na iran mai lakabin Operation True Promise III “zai ci gaba muddin akwai bukatar hakan,” yayin da ya sha alwashin daukar fansar jinin shahidai.
Tun da farko, Vahidi ya ce an kai hari a kalla wurare 150 a harin ramuwar gayya kan gwamnatin Isra’ila, ciki har da wasu sansanonin soji masu matukar muhimmanci.