Aminiya:
2025-04-30@23:19:27 GMT

An yi garkuwa da ɗan uwan ​​Bishop Kukah da wasu 6 a Kaduna

Published: 7th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane sun yi garkuwa da mutane bakwai da suka haɗa da mata da ƙananan yara a ƙauyen Anchuna da ke masarautar Ikulu a ƙaramar hukumar Zangon Kataf a Jihar Kaduna.

An samu rahoton cewa harin wanda ya auku a daren ranar Larabar, ya jefa al’ummar yankin cikin firgici yayin da maharan suka mamaye ƙauyen da suke da yawa, inda suka yi ta harbe-harbe kafin daga bisani su tafi da su.

Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa

Wani mazaunin yankin mai suna Samuel Kukah, ɗan gidan fitaccen malamin kirista, Bishop Hassan Kukah, ya tabbatar wa wakilinmu faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa akwai ƙaninsa Ishaya Kukah na cikin waɗanda aka kama.

“Yayana Ishaya, shi kaɗai ne namiji a cikin waɗanda aka sace; sauran mata da yara ne, maharan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 11 na dare,” in ji shi.

Kukah ya ƙara da cewa har ya zuwa lokacin da yake zantawa da wakilinmu, babu wata tuntuɓa da masu garkuwar suka yi dangane da neman kuɗin fansa.

“Muna yi musu addu’ar Allah ya kare su yayin da muke jiran kowane kira,” in ji shi.

Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ganin an dawo da waɗanda lamarin ya rutsa da su lafiya, yana mai jaddada cewa galibin waɗanda aka sace mutane ne masu rauni.

Da aka tuntuɓi jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya ce zai yi wa wakilinmu ƙarin bayani kan lamarin, amma har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ba.

Mazauna yankin na ci gaba da yin kira da a tsaurara matakan tsaro domin daƙile matsalar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran

Gwamnan lardin Hormozgan (mai hedikwata a Bandar Abbas), Mohammad Ashouri, ya ce wani bangare na lamarin tashar jiragen ruwa na Shahid Raja’i ya faru ne sakamakon keta sanarwar adana kayayyaki ne, wani bangaren kuma na da alaka da sakaci da rashin kulawa (a wajen ajiya).

AShouri, wanda ya bayyana ta hanyar faifan bidiyo a wata hira da aka watsa ta talabijin a yammacin jiya Litinin, ya bayyana sabbin alkaluman wadanda suka bata: Akwai mutanekusan 22 da suka bace, kamar yadda wasu gawarwakin mutane 22 ba a iya tantace su ba ko su waye ba.

Ya ce: “Wasu daga cikin wadanda suka jikkata an hanzarta jigilar su ta jirgin saman soja zuwa asibitin birnin Shiraz.”

Gwamnan lardin Hormozgan na Iran ya ce: An cimma wasu bincike na farko dangane da yiyuwar yin sakaci a wannan fanni, kuma ana gudanar da bincike sosai kan dukkan al’amuran da suka faru. Kuma babu wata daga kafa da za a yi ga duk wanda aka samu da yin sakaci a kan haka za a tuhume shi kamar yadda shari’a ta tanada.

 Ya ci gaba da cewa, “Ta hanyar nazarin faifan bidiyo daban-daban na aukuwar lamarin tashar jirgin ruwa ta Shahid Raja’i, an lura da cewa, an yi jigilar kaya a lokacin da lamarin ya faru, inda hayaki ke tashi, sai kuma fashewar wani abu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar