HausaTv:
2025-05-23@04:39:24 GMT

Saudiyya Za Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Amurka Da Ukiraniya

Published: 7th, March 2025 GMT

Shugaba Zelensky   na Ukiraniya zai kai ziyara kasar Saudiyya a ranar Litinin, gabanin bude tattaunawar da za a yi tsakanin kasarsa da kuma Amurka da zummar kawo karshen yaki da Rasha.

Shugaban na kasar Ukiraniya ya wallafa wani sako a shafinsa na X cewa; Manufar ziyarar tashi ita ce haduwa da yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman, sannan kuma tawagar da zai je da ita, za ta ci gaba da zama a can Saudiyya din saboda yin aiki tare da mutanen Saudiyya da kuma Amurka.

Zelensky ya kara da cewa; Kasarsa Ukiraniya tana son ganin an sami zaman lafiya mai dorewa.

Bugu da kari shugaban na kasar Ukiraniya ya ce; Matakin farko da kasarsa ta gabatar a matsayin shawarar kai wa ga zaman lafiya, shi ne dakatar da yaki a lokaci mafi kusa, da hakan zai zama share fage ne na warware sabanin da ake da shi baki daya,kuma Ukiraniya a shirye take ta yi aiki da Amurka a turai domin shimfida zaman lafiya”

Dangane da taron da za a yi a kasar Saudiyya, wani babban jami’in gwamnatin kasar ta Ukiraniya ya ce, a ranar Talata mai zuwa za a yi ganawa a tsakanin tawagar kasarsa da kuma ta Amurka a Saudiyya.

Jami’in na Ukiraniya ya ce ganawar za a yi ta ne a kokarin kyautata alaka a tsakanin kasashen biyu, bayan abinda ya faru na cacar baki a tsakanin Donald Trump a Zylenisky.

A gefe daya ministan tsaron Birtaniy John Healey ya furta cewa; Da akwai kyakkyawar dama ta tarihi domin shimfida zaman lafiya a Ukiraniya” sannan ya kara da cewa: “ Shugaban kasar Ukiraniya a shirye yake ya rattaba hannu akan yarjejeniya da Amurka, amma yana da bukatuwa da a ba shi lamuni.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Ukiraniya ya zaman lafiya a Ukiraniya

এছাড়াও পড়ুন:

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni

Sakataren harkokin wajen Amurka ya bayyana cewa: Gwamnatin rikon kwaryar Siriya na iya rugujewa cikin ‘yan makonni

Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa: Gwamnatin rikon kwarya a Siriya na iya rugujewa cikin ‘yan makwanni, lamarin da zai sa kasar ta fada cikin yakin basasa matukar Amurka ba ta ba ta hadin kai ba.

A yayin zaman Majalisar Dattijan Amurka, Sakataren harkokin wajen kasar Rubio ya yi furuci da cewa: Idan Amurka ta yi aiki da gwamnatin Siriya, yana iya yiwuwa, gwamnatin ta samu nasara, ko kuma gwamnatin ta kasa samun nasara idan Amureka ba yi aiki da ita ba, kuma tabbas ba zata taba samu nasara ba.

Ya kara da cewa: “A hasashen Amurka, idan aka yi la’akari da kalubalen da ake fuskanta, gwamnatin rikon kwaryar Siriya “watakila a ‘yan makwanni, ba watanni ba, da yiwuwar durkushewarta da kuma bullar yakin basasa, wanda gaba daya zai haifar da wargajewar kasar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Duniyarmu A Yau: Kan Tattaunawar Iran Amurka
  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin ZamfaraBabu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa Babu Wata Kyakkyawar Fata A Tattaunawar Iran Da Amurka
  • Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • Tattaunawar Iran da Amurka na inganta zaman lafiya a yankin : Araghchi