Aminiya:
2025-11-03@04:07:46 GMT

Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa

Published: 7th, March 2025 GMT

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe mayaƙan Boko Haram tara, ciki har da ƙwararren mai haɗa wa ƙungiyar bama-bamai, Amirul Bumma a wani samame da suka kai a dajin Sambisa da ke Jihar Borno.

Majiyoyi sun bayyana cewa sojojin sun kai farmakin ne a Ƙaramar Hukumar Bama, ƙarƙashin rundunar Operation Desert Sanity 4, bayan samun bayanan sirri.

Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha Doyin Okupe: Tsohon kakakin shugaban ƙasa ya rasu

Boko Haram sun yi ƙoƙarin tsayawa da su fafata, amma sojojin sun yi nasarar fatattakar su.

Bayan kammala artabun, mayaƙan sun dawo wajen da gadajen asibiti domin kwashe waɗanda suka jikkata, wanda hakan ke nuna girman asarar da suka yi.

Daga cikin waɗanda aka kashe akwai babban jagoran Boko Haram, Amirul Bumma tare da wasu manyan kwamandoji kamar Bakura Ghana, Awari, Malam Kalli, Malam Usman Bula Kagoye, da Ibrahim Bula Abu Asma’u.

Hakazalika, sun kashe wasu biyu da ba a tantance sunansu ba.

Har ila yau, sojojin sun ƙwato muggan makamai daga hannunsu.

A wani yunƙuri na ramuwar gayya, Boko Haram sun dasa bama-bamai a hanyar da sojojin suke bi, amma dakarun sun gano nufinsu tare da cire bama-bamai.

Babban Kwamandan runduna ta 7, Manjo Janar Abubakar Haruna, ya yababwa sojojin bisa wannan gagarumar nasara, da suka samu.

Ya jaddada cewar za su ci gaba da yaƙi da ta’addanci har sai an kawo ƙarshensa a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Artabu bayanan sirri hari Mayaƙan Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari

Naurorin tauraron dan adam sun nuna hoton yadda sojojin Amurka suke kara kusantar kasar venuzuwela ciki har da jiragen yaki masu kai hare-hare duk da yake cewa shugaban Amurka Dolad trump ya karyata batun da ake yi na yunkurin kai mata harin soji,

Wannan matakin yana daya daga cikin yadda sojojin ruwan Amurka suka mayar da hankali a yankin karebiya, wanda hakan ya haifar da damuwa a latin Amurka game da yiyuwar daukar matakin soji na bangare daya kan kasar Venuzuwela ba tare da izinin majalisar dinkin duniya ko kuma kasashen duniya ba,

Washington ta yi ikirarin cewa za ta kai hari kan masu fataucin miyagun kwayoyi ne sai dai masu sa ido kan alamuran yankin sun bayyana cewa yanayin yadda ake turawa da sojoji da makamai a yankin  yana nuna shirin da ake yi ne na daukar matakin soji ko kuma matsin lamba kan gwamnati venuzuwela don ta mika wuya.

Ana sa bangaren shugaban kasar venuzuwela yayi kira ga kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya da ya dauki mataki kan harin da Amurka ta kai kan wasu jirage dake kusa da ita a matsayin haramtacce kuma ta kare yancin kasar venuzuela

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari