Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa
Published: 7th, March 2025 GMT
Dakarun Sojin Najeriya sun kashe mayaƙan Boko Haram tara, ciki har da ƙwararren mai haɗa wa ƙungiyar bama-bamai, Amirul Bumma a wani samame da suka kai a dajin Sambisa da ke Jihar Borno.
Majiyoyi sun bayyana cewa sojojin sun kai farmakin ne a Ƙaramar Hukumar Bama, ƙarƙashin rundunar Operation Desert Sanity 4, bayan samun bayanan sirri.
Boko Haram sun yi ƙoƙarin tsayawa da su fafata, amma sojojin sun yi nasarar fatattakar su.
Bayan kammala artabun, mayaƙan sun dawo wajen da gadajen asibiti domin kwashe waɗanda suka jikkata, wanda hakan ke nuna girman asarar da suka yi.
Daga cikin waɗanda aka kashe akwai babban jagoran Boko Haram, Amirul Bumma tare da wasu manyan kwamandoji kamar Bakura Ghana, Awari, Malam Kalli, Malam Usman Bula Kagoye, da Ibrahim Bula Abu Asma’u.
Hakazalika, sun kashe wasu biyu da ba a tantance sunansu ba.
Har ila yau, sojojin sun ƙwato muggan makamai daga hannunsu.
A wani yunƙuri na ramuwar gayya, Boko Haram sun dasa bama-bamai a hanyar da sojojin suke bi, amma dakarun sun gano nufinsu tare da cire bama-bamai.
Babban Kwamandan runduna ta 7, Manjo Janar Abubakar Haruna, ya yababwa sojojin bisa wannan gagarumar nasara, da suka samu.
Ya jaddada cewar za su ci gaba da yaƙi da ta’addanci har sai an kawo ƙarshensa a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Artabu bayanan sirri hari Mayaƙan Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya sheƙar da ’yan siyasa daga ɓangarori daban-daban suke yi.
A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa Jam’iyyar APC mai mulki ta jawo ɗiga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaɓen 2027.
Hakan dai yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu ’yan ƙasar suke kokawa bisa yadda ake gudanar da mulki da kuma yadda wasu manyan ’yan siyasa suke fadi-tashin kafa wata inuwa da suka ce za ta ciro wa talaka kitse a wuta ta hanyar kawar da gwamnatin APC.
NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaWannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai da nufin gano alƙiblar da siyasar Najeriya take shirin fuskanta.
Domin sauke shirin. Latsa nan