Shugaban kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN Ali Muhammad Ali ya ce manyan taruka biyu na kasar Sin wato taron NPC da CPPCC sun zama muhimmiyar hanya ta fahimtar manufofin da gwamnatin Sin ke dauka da yadda take daidaita harkokinta da basirarta na zamanantar da al’ummar Sinawa.

Ali Muhammad ya bayyana haka ne yayin hirar da ya yi da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, inda ya kara da cewa, “Da farko mun zura ido kan nagartattun manufofin da Sin take dauka na daidaita harkokinta, wadanda tarukan biyu suka gabatar da su da sakamakon da take samu dangane da hakan a fili, manufofi kuma sun sauke nauyin dake wuyansu.

Musamman ma a halin da duniya ke ciki na fuskantar manyan sauye-sauye, dabaru da basirar Sin sun zama abin koyi.”

Sojoji Sun Kashe Ƙwararren Mai Haɗa Wa Boko Haram Bam A Borno Lamine Yamal Ya Amince Da Sabon Kwantiragi A Barcelona

Ya kara da cewa, “Ci gaban da Sin take samu na jawo hankulan kasashen Afirka matuka a halin yanzu, saboda ya samar da damammaki masu kyau. Huldar Sin da Afirka wadda ta kara zurfafa na inganta hadin gwiwar kasashe masu tasowa da samar da saurin bunkasuwa, haka ma ya gaggauta fahimta a tsakaninsu da hadin gwiwarsu.”

A cewarsa, yana fatan tarukan biyu za su fitar da karin sakon hadin gwiwar Afirka da Sin. Ya ce, “Ba ci gaban daidaita harkokinta dake jawo hankulan kasa da kasa take samu kawai ba, har ma tana gabatar da damammaki ga duniya bisa ra’ayin bude kofa da hakuri da juna. Ina fatan kasashen Afirka za su koyi basira da dabarun Sin ta hanyar zurfafa hadin gwiwarsu, ta yadda za a daidaita harkokin duniya da wadatar da duniya baki daya.” (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna

Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama mutane 11 da ake zargi da aikata damfara a Intanet a Jihar Kaduna.

Kakakin hukumar EFCC, Dele Oyewale, ya bayyana cewa an kama waɗanda ake zargin ne a unguwannin Mahuta da Barnawa bayan samun sahihan bayanai game da ayyukansu na yaudara ta yanar gizo.

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

A lokacin da aka kama su, EFCC ta ƙwace wasu kayayyaki daga hannunsu da suka haɗa da mota ƙirar Mercedes Benz C300 mai launin baƙi, wayoyi 14, kwamfutoci guda biyu, iPad, na’urorin mifi guda biyu, lasifikar JBL guda ɗaya, da kuma lasifikar zealot guda ɗaya.

EFCC ta ce za a gurfanar da su gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna