“Wannan kasafin kuɗin ya nuna sabon gagarumin fifiko a kan harkar tsaro, ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, ma’adanai, noma, da sauran sassa masu matuƙar tasiri kan jin daɗin al’umma da cigaban tattalin arzikin su.”

 

Ya ƙara da cewa shekarar 2025 ita ce “shekarar tabbatar da cigaba,” inda sauye-sauyen da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta fara aiwatarwa za su fara haifar da ainihin sauyi ga al’umma.

 

Ya kuma jaddada cewa tun tuni aka fara ganin sauƙin farashin kayan abinci, wanda ke samar da sauƙin rayuwa ga ‘yan ƙasa.

 

Ministan ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiwatar da kasafin kuɗi yadda ya kamata domin tabbatar da ingantaccen tasirin sa a rayuwar ‘yan Nijeriya.

 

Ya ce, “Ina tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa Gwamnatin Tarayya za ta yi aiki tuƙuru don ganin an aiwatar da kasafin kuɗi cikin tsari domin ya haifar da gagarumin tasiri a rayuwar al’umma. Saboda haka, ina kira ga ‘yan Nijeriya da su mara wa wannan ƙoƙari baya domin gina ƙasa mai cigaba da haɗin kai.”

 

Haka nan, Idris ya jinjina wa ‘yan jarida kan rawar da suke takawa wajen bayar da rahotanni na gaskiya da suka shafi cigaban ƙasa.

 

Ya buƙace su da su ci gaba da gudanar da aikin jarida bisa ƙa’idojin da suka dace domin ƙarfafa dimokiraɗiyya da inganta sanin makamar gwamnati a tsakanin al’umma.

 

“A wannan zamani da ƙarya ke yawaita wajen ruɗar da jama’a, jajircewar ku kan gaskiya da adalci ta fi zama dole fiye da kowane lokaci. Dole ne mu haɗa kai domin tabbatar da cewa labaran da ke tsara yadda ake tattauna batutuwan jama’a sun kasance bisa haƙiƙanin gaskiya, ba tare da son zuciya ko ƙazafi ba,” in ji shi.

 

Taron ya samu halartar Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dr. Jumoke Oduwole, da Ƙaramin Ministan ma’aikatar, Sanata John Owan Enoh, da wasu jigajigan gwamnati.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba

 

Ministan Ƙasa na Ci Gaban Yankuna, Uba Maigari Ahmadu, ya yaba wa ci gaba da tattaunawa tsakanin jami’an gwamnati da shugabannin arewa yana mai cewa wannan “tattaunawa ce mai tarihi kuma cike da ƙarfi,” yana nuna cewa hangen nesa na Shugaba Bola Tinubu ga Arewa ya fara samo asali kuma yana haifar da sakamako.

 

Yayin jawabi a taron gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello a rana ta biyu na zaman tattaunawa tsakanin gwamnati da alumma, ministan ya jaddada cewa wannan zama shi ne karo na farko a tarihin mulkin Najeriya inda ministoci, daraktocin hukumomi, shugabannin kwamitoci, da sauran manyan jami’an gwamnati daga Arewa suka “mika kansu don a yi musu tambayoyi” daga mutanen da suke yi wa hidima.

 

Ya ce gwamnati na da rubutattun nasarori da ake iya gani, yana bayyana wannan mataki a matsayin sabon hanya don samun amincewar jama’a, “wadanda su ne a ƙarshe suka fi rinjaye wajen zabe.”

 

Tattaunawar ta shafi fannoni da dama – tsaro na abinci, noma, ilimi, lafiya da ci gaban ababen more rayuwa – inda mahalarta suka amince cewa wadannan matsaloli suna da alaƙa sosai kuma suna bukatar kulawa cikin gaggawa.

 

Ministan ya bayyana wannan zama a matsayin “tattaunawar fannoni daban-daban don makomar Arewa,” yana mai cewa burin shi ne samar da tsare-tsare masu amfani ga birane da karkara.

 

Lokacin da aka tambaye shi yadda “hanyar gaba” za ta kasance, Ahmadu ya ce manufar gwamnati ba kawai yin magana ba ce, amma ta saurara, ta yi rubutu, kuma ta yi aiki.

 

Ya kara da cewa gwamnati na mai da hankali sosai kan batun sarƙoƙin samar da abinci, farfaɗo da noma da kare ‘yancin al’ummomin makiyaya.

 

A matsayin abin da ya kira “juyin hali,” Ahmadu ya tabbatar cewa gwamnati ta amince da karin kasafin kuɗi don shirye-shiryen ci gaban Arewa – abin da ya nuna gwamnati ba kawai alkawari take yi ba, har ma tana saka kuɗi a bayansa.

 

Sai dai ministan bai boye kalubalen da ke akwai ba, ciki har da matsin tattalin arziki, rikicin al’adu da harsuna, da ƙarin matsa lamba kan ƙasar noma saboda sauyin yanayi da yawaitar jama’a.

 

Ahmadu ya jaddada cewa wannan lokaci “sabuwar farawa” ce ga Arewa, wadda ke buƙatar haɗin kai tsakanin shugabanni, al’umma da hukumomin gwamnati.

 

Taron zai ci gaba na wasu kwanaki, inda za a gabatar da ƙarin rahotanni daga ma’aikatun gwamnati da hukumomi kamar North-East Development Commission don bayyana ci gaban ayyuka.

 

“Wannan abu ne game da gaskiya, amana, da sabuwar farawa ga Arewa,” in ji Ahmadu, yana tabbatar da cewa tattaunawar da ake yi yanzu za ta tsara makomar yankin.

 

COV: Khadija Kubau

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa