Aminiya:
2025-07-31@12:46:34 GMT

Ya rasu a yayin buɗa-baki a Abuja

Published: 3rd, March 2025 GMT

Wani mutum wanda aka bayyana a matsayin Abdulrashid Usman, ya yanke jiki ya mutu a yayin da yake buɗa-baki a yankin Babban Birnin Tarayya.

Wani shaida mai suna Suleiman Bala, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar da aka ɗauki azumi, lokacin da mamacin da abokansa suke buɗe-baki a majalisarsu da ke yankin Kutunu a Ƙaramar Hukumar Gwagwalada.

Ya ce Usman da abokansa suna zaune a kan benci suna cin ’ya’yan itatuwa ne ya yanke jiki ya faɗi, rai ya yi halinsa.

Nan take abokan suka garzaya da shi zuwa asibiti, inda likita ya tabbatar cewa rai ya yi halinsa.

A cewarsa, marigayin, wanda yake cikin koshin lafiya, ya dawo daga Kaduna ganin buɗa-baki, daga nan ya je majalisarsu ya haɗu da abokansa, bayan an sha ruwa suna tsaka da buɗa-baki lamarin ya faru.

“Wani ɗan uwan marigayin ya ce mamacin ya dawo daga Kaduna kuma ya je shiga cikin abokansa inda suke annashuwa.

“Bayan kiran Sallah suna buɗa-baki lamarin ya faru,” in ji shaidar.

Ya ce an binne shi bisa tsarin addinin Musulunci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buɗa baki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Ahmed Makama Hardawa, ya rasu.

Marigayin ya rasu ne ranar Talata a Abuja, bayan ya yi fama da gajeruwar jinya.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ne ya tabbatar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

Muna tafe da karin bayani…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON