HausaTv:
2025-05-22@13:57:33 GMT

Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan

Published: 2nd, March 2025 GMT

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres na mika sakon gaisuwa a yayin da al’ummar Musulmi a fadin duniya suka fara gudanar da azumin watan Ramadan.

Ramadan yana kunshe da dabi’u na tausayi, tausayawa da karamci. Sannan dama ce ta sake haduwa da dangi da sauran al’umma.

Kazalika dama ce ta tuna wadanda ba su samu damar sake ganin watan ba.

Ga duk wadanda suka samu ganin wannan lokaci mai tsarki cikin halin gudun hijira da tashin hankali, ina so in bayyana sakon tausayawa a gare su.

Ina goyon baya ga duk wadanda ke cikin halin tsanani da wahala, tun daga Gaza da sauran yankuna, zuwa Sudan, Sahel da sauran su. Kuma ina mai ba da hadin kai da masu gudanar da Azumin watan Ramadan da yin kira ga zaman lafiya da mutunta juna. A duk watan Ramadan, na kan kai ziyarar hadin kai tare da yin Azumi tare da al’ummar Musulmi a fadin duniya.

 Wadannan ayyuka suna tunatar da duniya hakikanin fuskar Musulunci. Kuma ko da yaushe na kan zama mafi samun kwarin gwiwa da kwanciyar hankali a wannan lokaci.

A cikin wannan wata mai alfarma, dukkkanmu muna samun daukaka ta hanyar dabbaka wadannan dabi’u kuma muna rungumar ‘yan uwantaka don gina duniya mai adalci da zaman lafiya ga kowa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: watan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba

Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta sanar da dakatar da duk wani nau’in tallan magungunan gargajiya a cikin fina-finai, a kan titi ko amfani da lasifika.

Wannan na cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, wadda Jami’in Yaɗa Labaran Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya raba wa manema labarai.

’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja

Shugaban hukumar ya ce wannan matakin na da nufin kare martabar masana’antar fina-finai da kuma tabbatar da cewa duk wani bayani da ke zuwa ga jama’a ya bi ƙa’idoji da doka.

“Yawancin tallace-tallacen maganin gargajiya da ake yi a tituna ko kuma a cikin fina-finai suna karya dokokin da hukumarmu ta gindaya.

“Wannan dalili ne ya sa muka ɗauki matakin dakatar da duk wata hanya da ake amfani da ita wajen wannan talla, har sai mun tantance su tare da bayar da sahalewa,” in ji El-Mustapha.

Hukumar ta bayyana cewa daga ranar Laraba, 21 ga watan Mayu, 2025, duk masu ruwa da tsaki a harkar maganin gargajiya dole ne su miƙa tsarin tallace-tallacensu domin tantancewa cikin mako guda, ko kuma su fuskanci hukuncin hukumar.

“Mun bai wa kowa kwana bakwai ya gabatar da tsarin tallarsa domin mu duba.

“Wannan ya shafi masu fina-finai da kuma waɗanda ke yawo da lasifika a titi. Doka za ta ɗauki mataki a kan duk wanda ya saɓa,” cewar El-Mustapha.

A cikin wannan sanarwar, shugaban hukumar ya kuma buƙaci haɗin gwiwar tashoshin talabijin da Hukumar Kula da Kafafen Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC), domin ganin an daƙile abin da ka iya shafar tarbiyya da lafiyar al’umma.

“Muna kira ga tashoshin talabijin da hukumar NBC su mara mana baya wajen tabbatar da bin doka da oda a fannin yaɗa bayanai, musamman masu nasaba da magunguna da lafiya. Wannan zai taimaka wajen kare martabar fina-finai da kuma lafiyar al’umma,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin jiragen sama sun tsawaita dakatar da zirga-zirgar zuwa Isra’ila
  • Sojojin HKI Sun Bude Wuta Kan Jami’an Diblomasiyyar Wadanda Suka Je Jenin
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • Xi Ya Jaddada Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaba Mai Inganci A Kasar Yayin Ziyararsa A Henan 
  • Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin SCO Na 2025
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa
  • Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15
  • Fahimtar Hakikanin kasar Sin
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Bisa Daidaito A Afirilu