HausaTv:
2025-07-07@11:35:10 GMT

Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan

Published: 2nd, March 2025 GMT

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres na mika sakon gaisuwa a yayin da al’ummar Musulmi a fadin duniya suka fara gudanar da azumin watan Ramadan.

Ramadan yana kunshe da dabi’u na tausayi, tausayawa da karamci. Sannan dama ce ta sake haduwa da dangi da sauran al’umma.

Kazalika dama ce ta tuna wadanda ba su samu damar sake ganin watan ba.

Ga duk wadanda suka samu ganin wannan lokaci mai tsarki cikin halin gudun hijira da tashin hankali, ina so in bayyana sakon tausayawa a gare su.

Ina goyon baya ga duk wadanda ke cikin halin tsanani da wahala, tun daga Gaza da sauran yankuna, zuwa Sudan, Sahel da sauran su. Kuma ina mai ba da hadin kai da masu gudanar da Azumin watan Ramadan da yin kira ga zaman lafiya da mutunta juna. A duk watan Ramadan, na kan kai ziyarar hadin kai tare da yin Azumi tare da al’ummar Musulmi a fadin duniya.

 Wadannan ayyuka suna tunatar da duniya hakikanin fuskar Musulunci. Kuma ko da yaushe na kan zama mafi samun kwarin gwiwa da kwanciyar hankali a wannan lokaci.

A cikin wannan wata mai alfarma, dukkkanmu muna samun daukaka ta hanyar dabbaka wadannan dabi’u kuma muna rungumar ‘yan uwantaka don gina duniya mai adalci da zaman lafiya ga kowa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: watan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Mufti Na Masarautar Oman Ya Yi Kakkausar Suka Kan Masu Son Kulla Alaka Da H.K.Isra’ila

Babban Mufti na masarautar Oman ya yi kakkausar suka kan kasashen da ke neman kulla alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila

Babban Mufti na masarautar Oman, Sheikh Ahmed bin Hamad Al-Khalili, ya bayyana mamakinsa kan yadda wasu kasashe ke son kulla                     alaka da makiya yahudawan sahayoniyya, wata kasa ‘yar mamaya maras tushe.

A cikin wani bayani da ya wallafa a shafinsa na X, Ahmed bin Hamad Al-Khalili ya ce: “Abin mamaki ne yadda wasu kasashe ke son kyautata alaka da makiya yahudawan sahayoniyya, alhali su kansu suna kallon wannan mahalukiya a matsayin wata kasa mai gushewa ko ba dade ko ba jima, al’ummarta dai suna son ci gaba da yakin ne kawai don ci gaba da wanzuwarta, in ba haka ba, babu wanda a can yake son ci gaba da zama a wannan kasa bayan sun ga cewa hakan ba ya cikin maslahar rayuwa.”

Al-Khalili ya ce: “Ta yaya wadanda suke da tushe zasu kulla alaka da gwamnati da zata gushe da hukuma wacce zata gushe ko ba dade ko ba jima.?

Babban Mufti na masarautar Oman ya kara da cewa: “Idan kana son sanin girman bala’i da girman masifa, to ka yi tunanin yadda alakarka zata kasance da mai dabi’ar dabbobi mai kashe fararen hula daga yara da mata da kuma tsofaffi, ta yaya zai kare maka naka hakkokin?  Ya karkare bayanin da cewa: “Mutum ya halaka a cikin kwanakinsa na jarrabawa…idan baya iya bambance tsakanin mai kyau da maras kyau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sheikh Ibrahim Zakzaky Ya Taya JMI Murnar Nasara A Kan Mikiyanta
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Babban Mufti Na Masarautar Oman Ya Yi Kakkausar Suka Kan Masu Son Kulla Alaka Da H.K.Isra’ila
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata
  •  Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila
  • Miliyoyin Iranauawa Sun Fito Makokin 8 Ga Watan Muharram
  • In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba